Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Ƙa'idojin alaƙa tsakanin jinsi biyu (Na miji da ta mace)

A cikin wannan darasin zaka san ƙa'idojin alaƙa tsakanin na miji da ta mace.

  • Gabatarwa akan mahimmancin lizimtar ƙa'idojin shari'a wacce take hukunta alaƙar dake tsakanin na miji da ta mace. 
  • Bayanin adadi da yawa na daga ƙa'idojin sharia wajen mu'amalar na miji da mace. 

Shari’ar Musulunci ta kula da tsara al’amuran mutane a fagage daban-daban, ciki har da ɓangaren mu’amala tsakanin maza da mata. Allah Ta’ala ya halicci maza da mata da sha’awar juna, kuma sakamakon wannan sha’awar abu ne kyakkyawa kuma halal ne ta hanyar aure. Kuma duk wani abin da ba haka ba, ƙofa ce zuwa ga sharri da fitina, ɗaya daga cikin fitintinu masu tsanani. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Ban bari a bayana wata fitinar da ta fi mata illa ga maza ba. (Al-Bukhari 5096, da Muslim 2741).

Lalle mafi hatsarin sakamakon dangantaka tsakanin namiji da mace shi ne zina. Kuma shari’ar Musulunci bata taƙaita kawai da haramta wannan zunubi ba, sai dai, tana kuma gargaɗi da ko kusantarsa kada ayi kuma a nisanci duk wani abu da zai iya kaiwa zuwa gare shi. Allah maɗaukaki yana cewa: {Kuma kada ku kusanci zina. Lalle ne ita ta kasance alfasha ce, kuma tafarkinta ya munana.} [Isra'i: 32]. Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “Ido suna yin zina da kallo, kunne da saurare, harshe da magana, hannu da kamawa, ƙafa da tafiya, zuciya da sha’awa, al’aura kuma sai ta tabbatar da haka ko kuma ta ƙarya ta shi”. (Bukhari 6243, Muslim 2657, kuma lafazin nasa ne).

Saboda damuwa da kiyaye duk wata karkata ko kuskure da kan iya haifar da mummunan sakamako, shari'ar Musulunci ta tsara wasu tsare-tsare na mu'amalar maza da mata a cikin yanayi na larura, kamar saye, sayarwa, da sauran mu'amalolin da suka halatta, ko kuma a wani yanayi na larura, kamar macen da take neman magani daga wurin likita namiji a lokacin da mace likita ba ta samu ba. Waɗannan ƙa'idojin sun haɗa da:

Runtsa Idanu

Allah Ta’ala ya ce: {Ka ce wa muminai maza su runtse daga ganinsu, kuma su tsare farjojinsu. Wancan ne mafi tsarki a gare su. Lalle ne Allah, ga abin da suke aikatãwa Masani ne. (30) Kuma ka ce wa muminai mata su runtse daga ganinsu, kuma su tsare farjojinsu.) [Nur: 30, 31].

Nisanta shafa ko musafaha

An karɓo daga Aisha Allah Ya kara mata yarda tace, yayin da take bayani akan mubaya’ar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ga mata: “Wallahi Hannun Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bai taɓa taɓa hannun mace ba” (Bukhari 5288, da Muslim 1866). An karɓo daga Ma’aƙal Ɗan Yasar Allah Ya yarda da shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Da za a soki ɗayanku a kai da alluran ƙarfe ya fi alheri a gare shi da ya shafi macen da ba ta halatta gare shi.” (Aɗ-ɗabaraniy a cikin Al-Kabir 486, kuma Albani ya inganta shi).

Nisantan dukkanin keɓanta

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Kada wani namiji ya keɓanta da wata mace face a gaban wani ɗan uwanta na kusa” (Bukhari 5233, da Muslim 1341). Kuma ya ce: “Kada ɗayanku ya keɓanta da mace, domin Shaiɗan ne na uku a wurin” (Ahmad: 115). Don haka keɓanta ƙofa ce zuwa ga ɓarna da ta'adi wacce Shaiɗan ke amfani da ita wajen kai maza da mata cikin abin da Allah Ya haramta.

Ƙa'idojin da suka keɓanta ga mace

Akwai wasu ƙa'idojin da ya wajaba mace musulma ta kiyaye su yayin da buƙatuwa ta kaita yin mu'amala da maza

Lizimtar tufafin shari'a

Wajibi ne mace musulma ta yi riƙo da ka'idojin suturar Musulunci, na farko domin biyayya ga umarnin Allah Maɗaukakin Sarki, na biyu kuma ta tilasta wa maza su girmama ta, kada su cutar da ita; ta aiki, zance, ko kallo. Allah Ta’ala ya ce: {Kuma ka ce wa muminai mata su runtse daga ganinsu, kuma su kiyaye farjojinsu, kuma kada su bayyanar da ƙawarsu face abin da ya bayyana daga gare ta, kuma su yi lulluɓi a kan ƙirjinsu} [Nur: 31]. Kuma Allah Maɗaukakin Sarki ya ce: {Ya kai Annabi ka ce wa matanka da ƴaƴanka mata da matan muminai su rufe kansu da tufafinsu. Wancan ne mafi cancantar a gane su, kuma kada a zãlunce su. Kuma Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin kai.} [Ahzab: 59].

Nisantar fesa turare a gaban maza

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “Duk macen da ta fesa turare sannan ta wuce ta kan wasu jama’a domin su ji ƙamshinta, to mazinaciya ce”. (An-Nasa’i 5126).

Magana da gaskiya da kuma barin sassauta zance

Allah Ta’ala ya ce: {Ya ku matan Annabi, ba ku zama kamar sauran mata ba. Idan kun bi Allah da taƙawa, to, kada ku sassauta magana (ga mutane), har wanda a cikin zuciyarsa akwai cuta ya yi kwaɗayin ku, kuma ku yi zance da magana mai kyau.} [Ahzab: 32].

Tafiya cikin kunya da tsanaki

Allah Ta’ala ya ce game da ƴar Annabi Shu’aibu a lokacin da ta je wajen Annabi Musa, domin isar da saƙon babanta zuwa gare shi: {Sai ɗaya daga cikin matan biyu ta zo masa tana tafiya cikin ladabi} [Qasas: 25]. Kuma Allah Ta’ala ya ce, yana magana da mata: {Kuma kada su buga ƙafofinsu, domin su bayyana abin da suke ɓoye na daga adonsu} [Nur: 31].

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa