Zakkah
Zakkah ita ce rukuni na uku daga cikin rukunnan musulunci, kuma ita wajibi ne na dukiya wanda Allah Ya farlanta wa masu kuɗi domin su baiwa talakawa da mabuƙata da wasunsu na daga waɗanda suka cancanci wani kashi na musamman daga dukiyarsu domin magance matsalolinsu.