Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Ladduban neman aure

A cikin wannan darasin zamu san abunda ake nufi da neman aure da wasu daga cikin laddubanshi.

  • Gabatarwa akan abunda ake nufi da neman aure. 
  • Bayani akan wasu daga cikin ladduban neman aure a Musulunci. 
  • Bayyana wasu kyawawan ababe na Musulunci waɗan da suke da alaƙa da neman aure. 

Neman Aure shi ne mutum ya sanar da waliyyin mace cewa lalle shi yanada buƙatar aurenta a bisa sunnar Allah da kuma sunnar ManzonShi (S. A. W).

Yana daga cikin ni'imomin Allah Maɗaukakin Sarki cewa Ya tsara laduban neman aure, waɗanda za su samar da gamsuwa, da kyakkyawan zaɓi da da natsuwa, kuma zasu taimakawa kowane daga ma'auratan da su kasance cikin fahimtar juna da jituwa da juna.

Daga cikin ladduban neman Aure

1- Kada ya nemi aure a bisa neman ɗan uwanshi musulmi, Manzon Allah (S. A. W) yace: «Kada mutum yayi ciniki a bisa cinikin ɗan uwanshi, kuma kada ya nemi aure a bisa neman ɗan uwanshi sai dai idan shi ya ba shi izini.(Bukhari: 5142, Muslim: 1412).

2- Kallon matar da ake so a aura, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace wa Mughirah Ɗan Shu’bah a lokacin da ya ke so ya auri wata mata: “Ka kalle ta, domin lallai hakanne mafi kusantar samun jituwa a tsakaninku” (At-Tirmizi 1087). Kallon wanda za a aura shima haƙƙi ne na mace, har ma wasu malamai suna ganin cewa mace ita tafi cancanta ma da kallon wanda yake son auranta. Ma'anar "don samar da jituwa a tsakaninku" shi ne: Domin haifar da soyayya mai ɗorewa a tsakaninku.

An karɓo daga Jabir Ɗan Abdullah, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Idan ɗayanku yana neman mace da aure, idan har zai iya ganin abin da zai ƙarfafa shi ya aure ta, to ya yi”. Ya ce: “Saboda haka na kasance ina neman wata budurwa, sai na kasance ina ɓuya ina kallonta har sai da na ga abin da ya ƙarfafa ni akan aurenta sai na aure ta.” (Abu Dawud 2082)

Daga cikin ladduban kallon wanda ake so a aura:

١
Kada mai neman auri ya kalla wanda yake so ya aura sai bayan ya tabbatar da cewa lalle yayi azama akan aurenta.
٢
Ya kasance ya kalle ta ne gabanin ya fara nemanta da aure, domin kada kallon ya cutar da ita idan har bata mishi ba.
٣
Ya halalta ya ganta sau da yawa har sai ya samu gamsuwa da kuma natsuwa akanta.
٤
Idan har buƙatarshi na daga kallonta ya biya, sai ya kame daga kallontan; domin har yanzu bata halalta a gare shi ba tukunna.

3- Daga cikin muhimman ladubban neman aure shi ne mace da namiji su yi zaɓi nagari, sannan su mayar da hankali kan ingantattun ginshiƙai waɗnda za su samar musu da gida wacce zata cika da natsuwa da jin daɗi da kuma kwanciyar hankali da yardan Allah.

4-Daga cikin ladubban neman aure akwai mutum ya kasance mai kwaɗayin ya auri mace mai haihuwa domin ƙara yawan zuriya ta gari, kamar yadda manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nasiha da cewa: "Ku auri mata waɗanda kuke so kuma masu haihuwa, domin lallai ni zanyi alfahari da yawan adadinku a cikin al'ummai" (Abu Dawud 2050).

5- Neman shawara da neman zaɓi da kuma addu'a. Musulmi yana neman zaɓin Ubangijinshi Maɗaukaki ne a koda yaushe kuma yana roƙonShi, kuma yana yin shawara da ma'abota hankali da hikima a cikin kowane hali. Kuma lalle yanke hukuncin yin aure wani babban lamari ne mai muhimmanci a cikin rayuwar mutum, saboda haka ne ya kamata yayi abin da ya dace ta fuskar tuntuɓa da neman shawara da kuma addu’a.

6- Dole ne dukkanin ɓangarorin biyu su kasance masu gaskiya da amana wajen bayyana dukkan al'amura da yanayi, ta yadda babu wani aibi da zasu ɓoye, ko kuma suyi amfani da ƙarya da gangan ko yaudara wacce za ta shafi alaƙar da ke tsakanin ɓangarorin biyu a nan gaba bayan aure.

7-Kiyaye hukunce-hukuncen shari’a da suka shafi neman aure, kasancewar wannan alƙawarin aure ne kawai ba auren kansa ba. Don haka musafaha, kaɗaitaka, yin magana cikin sassauta zance ko sanya turare da ado ga mai neman aure, bai halatta ba.

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa