Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Haƙƙokin Iyaye

A cikin wannan darasin zamu san ma'anar biyayya ga iyaye da kuma wasu hukunce-hukuncen da suke da alaƙa da shi.

  • Bayani akan girman matsayin iyaye a cikin Musulunci. 
  • Kwaɗaitarwa akan biyayya ga iyaye da kuma tsoratarwa daga saɓa musu. 
  • Gabatarwa akan mafi mahimmncin ababen da suka wajaba akan yara game da iyayensu. 
  • Bayanin wasu ladduba yayin mu'amalantar iyaye. 

Matsayin iyaye a Musulunci.

Musulunci ya girmama iyaye da mafi girman daraja, kuma ya haɗa kyautata musu da mafi girman al’amari a Musulunci, wanda shi ne kaɗaita Allah maɗaukaki. Allah Ta’ala ya ce: {Kuma Ubangijinku Ya hukunta kada ku bauta wa kowa face Shi, kuma ku kyautata wa iyayenku} [Isra’i: 23]. Allah Maɗaukakin Sarki Ya sanya iyaye su ne dalilin samuwar ƴaƴa maza da mata, kuma ko me ƴaƴa za su yi, ba za su iya biyan komai daga cikin falalar iyaye ba, ko saka musu wahala, da wuya, da cutarwa, da rashin barci, da tsayuwa, da rashin hutu da suka jure saboda jin daɗin ƴaƴansu, da kuma kula da su ba.

Kuma daga cikin adalcin Allah Maɗaukakin Sarki ne Ya wajabta wa iyaye haƙƙinsu a kan ƴaƴansu, a matsayin sakamako ga kyakkyawan ƙoƙarin da suka yi da kuma ci gaba da yi wajen kula da su. Allah Ta’ala ya ce: {Kuma mun yi wa mutum wasiyya da kyautatawa ga mahaifansa} [Ankabut: 8], kuma ya ce: {Kuma ka raka su a duniya da kyautatawa} [Luqman: 15]. Yayin da wani daga cikin Sahabbai ya tambayi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa: “Ya Manzon Allah, a cikin mutane wane ne ya fi cancanta da kyakkyawar abotata? Ya ce: "Mahaifiyarka." Ya ce: "To sai wanene?" Ya ce: "Sai mahaifiyarka." Ya ce: "To sai wanene?" Ya ce: "Sai mahaifiyarka." Ya ce: "To sai wanene?" Ya ce: "Sai babanka." (Al-Bukhari 5971, da Muslim 2548).

Falalan biyayya ga iyaye

Girmama iyaye wani aiki ne kuma wajibi ne akan ƴaƴa, kuma a cikin girmama su akwai sakamako mai girma da lada mai yawa. Shi ne sanadi na ni'ima, da arziki, da yalwar alheri a duniya, kuma sababin shiga Aljanna a Lahira. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Ya taɓe kuma yayi hasara, Ya taɓe kuma yayi hasara, ya taɓe kuma yayi hasara, Aka ce: Wanene wannan ya Manzon Allah? Sai ya ce: “Wanda ya sami mahaifansa da tsufa, ɗayansu ko su biyu, sa’annan bai shiga Aljanna ba.” (Muslim: 2551).

Tausasawa ga iyaye yana daga cikin mafifitan ayyuka kuma mafi soyuwa ga Allah. Abdullahi bin Mas'ud, Allah Ya yarda da shi, ya tambayi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: Wane aiki ne ya fi soyuwa a wurin Allah? Ya ce: "Sallah a kan ƙayyadadden lokaci." Ya ce: Sai me? Ya ce: "Sai kyautatawa iyaye." Ya ce: Sai me? Ya ce: "Jihadi a tafarkin Allah" (Bukhari 527, da Muslim 85).

Girmama iyaye ya fi yin jihadin nafila. Wani mutum ya zo wajen Annabi (SAW) ya ce: Shin in shiga jihadi? Ya ce: Kana da iyaye? Sai ya ce: Eh. Ya ce: To, kaje ka yi jihadi a cikin hidimarsu. (Al-Bukhari 5972, da Muslim 2549).

Saɓawa iyaye

Rashin biyayya ga iyaye yana daga cikin manya-manyan zunubai da munanan laifuka. A cikin hadisin, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Mafi girman zunubai shi ne shirka ga Allah da saɓa wa iyaye.” (Bukhari 6919, da Muslim 87).

Ababen da suke wajibi akan yara dangane da iyayensu

١
Ana son yin biyayya gare su a cikin abin da suke umurni da shi na alheri, matuƙar yana cikin iyakokin iyawar mutum. Amma idan suka yi umarni da saɓawa Allah, to ba za a yi musu biyayya a cikinsa ba, tunda babu biyayya ga halitta wajen saɓa wa Mahalicci.
٢
Ka yi tarayya da su da kyautatawa ko da sun zalunce ka. Kuma shin akwai wani zalunci mafi girma da ya kai kiransa zuwa ga shirka da azaba dawwamammiya a cikin wuta? Amma duk da haka Allah maɗaukaki ya ce: {Kuma idan suka yi nufin su sanya ka shirki da Ni da abin da ba ka da ilmi game da shi, to kada ka yi musu biyayya, kuma ka raka su a cikin duniya da kyautatawa} [Luqman: 15].
٣
Kula da su da kyautata musu, kuma ana yin haka ne ta hanyar samar musu da kowane nau'i na kyautatawa, hidima da biyayya, tare da ƙaunar su da kyautata mu'amala da su. Allah Ta’ala ya ce: {Kuma Ubangijinku Ya hukunta kada ku bauta wa kowa face Shi, kuma ku kyautata wa iyayenku} [Isra’i: 23].
٤
Kada ku cutar da su ko kaɗan, har ma da kalmar "Uff," musamman a lokacin tsufa. Allah Ta'ala ya ce: {Ko ɗayansu ya kai ga tsufa a tare da ku, to, kada ku ce musu "Uff," kuma kada ku wulaƙanta su, kuma ku gaya musu magana mai kyau " [Isra'i: 23].
٥
Ka sassauta fikafikanka, kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabansu, kamar yadda Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: {Kuma ka sassauta musu fikafikan tawali’u domin rahama, kuma ka ce: “Ya Ubangiji! Ka jiƙan su kamar yadda suka rene ni ina yaro ƙanƙani) (Isra'i: 24).
٦
Ci gaba da yi masu godiya da kuma yarda da falalarsu. Allah Ta’ala ya ce: {Kuma mun yi wasiyya ga mutum game da iyayensa. Mahaifiyarsa ta ɗauke shi a rauni akan rauni, da kuma yãyensa a cikin shẽkara biyu . Toh ku yi godiya gare Ni da mahaifan ku. zuwa gare Ni makoma take.} [Luqman: 14].
٧
Ciyar da su da kyautatawa. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Ku da dukiyoyinku na iyayenku ne, ƴaƴanku suna daga cikin mafi alherin abin da kuka samu, saboda haka ku ci daga abin da ƴaƴanku suke samu. (Abu Dawud 3530).
٨
Yi musu addu'a a rayuwarsu da bayan rasuwarsu. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Idan mutum ya mutu ayyukansa sun tsaya sai dai guda uku: Sadaka mai gudana, ko ilimin da ake amfana da shi, ko wani yaro na ƙwarai wanda yake yi masa addu’a. (Muslim 1631).
٩
Girmama abokan iyayen mutum bayan rasuwarsu. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Mafi alherin aikin alheri shi ne mutum ya ƙulla alaƙa da abokan babansa” (Muslim 2552).

Ladduban da suka wajaba wajen mu'amala da iyaye

١
Sauraren su da kyau da kuma kulawa da hirarsu, da barin shagaltuwa da wani abu yayin magana da su kamar wayar hannu ko wani abu na daban.
٢
Aikata abunda zai faranta musu gabanin su nemi shi, da kuma kiyaye abunda zai baƙanta musu kafin ya iso gare su.
٣
Saurin amsa ƙiransu, da kuma nuna yarda yayin amsawar ba tare da ɓata lokaci ba.
٤
Gabatar da nasiha cikin hikima da tausasawa a gare su yayin da suka faɗa cikin wani laifi.
٥
Fuskantar kaushin iyaye da zalumcinsu -Idan hakan ya faru- da haƙuri da kyautatawa da kuma girmamawa.
٦
Rashin taurin kai da bijirewa
٧
Yawan murmushi a gabansu.
٨
Yin shawara da su, da shigar da su cikin lamarin mutum, da kuma girmama ra'ayinsu.
٩
Kwaɗaituwa a bisa hira da zance da tattaunawa akan lammuran yau da kullum tare da su, idan har hakan yana burge su.
١٠
Yayin rabuwa da su saboda tafiya, ya wajaba akan yaro da ya dinga ƙiransu domin sanin yanayin da suke ciki.

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa