Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Haƙƙokin Yara

A cikin wannan darasin zamu san haƙƙokin yara akan iyayensu

  • Bayanin ni'imar Allah akan iyaye na basu Zurriyya. 
  • Bayanin himmatuwan tsarkakakkiyar shari'a akan tarbiyan yara. 
  • Gabatarwa akan mafi mahimmancin haƙƙokin yara akan iyaye. 

Allah Ya cusawa zukatan iyaye maza da mata son samun zuriya masu lafiya da inganci. Wannan ita ce fatar babanmu Annabi Adamu da matarsa, Sallallahu Alaihi Wasallama. Allah Ta’ala ya ce: {Shi ne wanda Ya halicce ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi, matarshi, dõmin ya natsu zuwa gare ta. Kuma a lõkacin da ya rufe ta (ya sadu da ita), sai ta yi ciki mara nauyi, kuma ta ci gaba a cikinsa. Kuma a lokacin da ya yi nauyi, sai suka ƙirayi Allah Ubangijinsu cewa: "Idan Ka ba mu ɗa nagari, to, lalle ne mu muna daga masu godiya" [A'araf: 189]. Kuma cikan wannan burin kawai wata ni'ima ce da falala daga Allah Maɗaukakin Sarki. wanda ya wajaba a gode mi Shi a bisa hakan a koda yaushe.

Musulunci ya himmatu da lamarin zurriyya da abin da ya shafe su, kuma daga cikin abunda yake nuni zuwa ga wannan maganan a cikin Alkur’ani mai girma game da mahimmancin zuriya da ni'imar ƴaƴa shi ne lalle Allah Ya yi magana akan hakan bayan magana game da mulkin Allah a kan sammai da ƙasa. Allah Ta’ala ya ce: (Mulkin sammai da ƙasa na Allah ne kawai. Yanã halitta abin da Yake so. Yanã bãyar da ɗiya mace ga wanda Yake so, kuma Yanã bãyar da ƴaƴa maza ga wanda Yake so. (49) Ko kuma Ya haɗa su maza da mãtã, kuma Yanã sanya wanda Yake so bakarãre (Wanda baya haihuwa). Lalle Shĩ Masani ne, Mai ĩkon yi. [Ash-Shura: 49-50] Kuma Allah Maɗaukakin sarki ya sanya zuriya a cikin adon rayuwar duniya, kamar yadda Shi Mai girma da ɗaukaka ya ce: (Dukiya da ƴaƴa ado ne na rayuwar Duniya) (Alkahfi: 64).

Shari’ar Musulunci ta ba ƴaƴa da tarbiyyarsu muhimmanci mai girman gaske, domin su ne ginshiƙin nan gaba, kuma ta hanyar nagartan su ne bautar Allah Maɗaukakin Sarki zata ci gaba a doron ƙasa, kuma za a raya kasa yadda Allah Maɗaukakin Sarki Ya keso. Allah Ta’ala ya ce: {Ya ku waɗanda suka yi imani, ku tsare kanku da iyalanku daga wuta wadda makamashinta mutane ne da duwatsu} [Tahrim: 6]. Ali Allah Ya yarda da shi ya ce: Wannan yana nufin ku koyar dasu, kuma ku ladabtar da su. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Duk wanda ya reni ƴaƴa mata guda biyu har sai sun balaga, ni da shi za mu zo ranar kiyama kamar haka,” sai ya haɗa yatsunshi wuri guda (Muslim 2631).

Haƙƙoƙin yara akan iyayensu

١
Haƙƙoƙi na zahiri.
٢
Haƙƙoƙi na ciki.

Haƙƙoƙi na zahiri

Waɗannan haƙƙoki sun haɗa da samar da wurin zama, da abinci, da abin sha, da tufafi, da kula da lafiya, da kashe kuɗi ga yara kamar yadda shari’ar Musulunci ta tanada. Kuma babu shakka Waɗannan haƙƙoƙi sun wajaba a kan uba idan har yana da iko.

Haƙƙoƙi na ciki

Daga cikin mafi girman haƙƙokƙin ciki wadɗanda suka wajaba akan iyaye dangane da yaransu shi ne ta da su a bisa nagartacciyar turba wacce take kan ingantattun ginshiƙan addini, sai su koya musu Alkur'ani mai girma da ingantacciyar sunnar Annabi, da tarihin rayuwar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma su rene su a bisa koyarwar musulunci ta hanyar aikata umarnin Allah da nisantar haninShi, da kuma lizimtar ababen dake cikinshi na kyawawan ɗabi'u, kuma wannan dukka yana cikin inuwar girmama Allah Mai girma da ɗaukaka da sonShi, da son AnnabinShi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da son addininShi da kuma shari'arShi.

Kyautatawa ga yara yana da matuƙar tasiri wajen tarbiyyar su da ci gaban hankalinsu, matukar hakan bai kai ga wuce gona da iri wanda zai kaisu ga lalaci a rayuwa ba. Saɓanin haka, rashin tausayi da kyautatawa ga yara, da mu'amalantarsu da muzgunawa da tozartawa, ko rashin kulawa da su, yana iya baƙanta musu ruhi, ya kashe hasken hankali a cikin zukatansu, ya jarabce su zuwa ga saɓawa iyaye, da tawaye haƙƙoƙinsu, da watakila ma fasadi da ɓarna.

Daga cikin haƙƙoƙin yara akan iyayensu akwai samar da yanayi na mutuntawa, natsuwa, kwanciyar hankali da ƙauna acikin iyali, ta yadda kada abar rigiman dake tsakanin iyaye ko manyan ƴan uwa ya cika gidan, domin hakan zai iya shafan ɗabi’un ƙananan yara ya kuma sanya su cikin ɗimuwa da tashin hankali.

Daga cikin manyan haƙƙoƙin yara akan iyayensu akwai sama musu abokai na gari da kuma rashin barinsu su cakuɗu da yara masu miyagun halaye ko munanan ɗabi'a domin hakan zaiyi tasiri a cikin halayensu.

Nasiha, da faɗakarwa, da kuma shiryarwa.

Ya kamata iyaye su dinga bibiyan yanayin ƴaƴansu maza da mata, su kuma kula da halayensu da ayyukansu, kuma su ba su shawara, su faɗakar da su, su shiryar da su a duk lokacin da akwai buƙatan hakan, kuma daidaito yana da mahimmanci a cikin hakan, domin bai kamata shiryarwa da faɗakarwan ya kasance a koda yaushe ba, kaman yadda bai kamata su kasance akan kowana abu ba. Domin wannan na iya sa yaron ya gaji ya kuma ƙosa da saurare ko aiki da shawaran; saboda haka ya kamata iyaye su zabi lokuta da hanyoyin da suka dace don ba da shawara ga ƴaƴansu da kuma faɗakar da su.

Haƙƙoƙin yara akan iyayensu

١
Haƙƙoƙin yara yana farawa ne tun gabanin haihuwansu; ta hanyar zaɓan mace ta gari ko miji na gari.
٢
Haƙƙin yara a cikin samuwa da rayuwa.
٣
Haƙƙin yara a cikin dangi.
٤
Haƙƙin yara a cikin shayarwa.
٥
Haƙƙin yara na zaɓa musu suna mai kyau.
٦
Haƙƙin yara na suna da yanka.
٧
Haƙƙin yara na mu'amala da adalci.
٨
Haƙƙin yara na yi musu Addu'a.

Zaɓan mace ta gari da miji na gari

Ya wajaba akan na miji da ya zaɓi macen da ya ke ganin cewa za ta zamto uwa ta gari, haka kuma mace ma ya wajaba a gare ta da ta zaɓi mijin da take kyautata zaton cewa zai zamto uba na gari.

Haƙƙin yara cikin samuwa da rayuwa

١
Shari'ar Musulunci ta haramta kashe yara, kuma wannan abu ne wanda aka kasance ana aikatawa a Jahiliyya domin tsoron talauci da kunya.
٢
Musulunci ya haramta kamewa gaba ɗaya daga haihuwa.
٣
Musulunci ya hana zubar da ciki da kuma rabuwa da yaro bayan an busa mishi rai.

Haƙƙin yara a cikin dangi

Kuma shi ne Haƙƙin yaro na danganta shi zuwa mahaifinshi, domin duk wasu haƙƙoƙin yara na bayyane da na ciki sun rataya ne akan wannan hakkin; Saboda haka ba ya halatta ga wani mutum da ya barranta daga wani yaro ko yayi inkarin dangantakan shi zuwa gare shi sai dai da hujjar da bata karɓan shakka.

Haƙƙin yara wajen shayarwar ɗabi'a

Kuma haƙiƙa ilimin zamani ya tabbatar da fa'idodi da dama na kiwon lafiya, da na hankali da tunani, na wannan shayarwa, kuma ita ce wacce tafi dacewa da buƙatan yaro da kuma garkuwan jikinshi, kuma ita ce zata kyautata gina shi ta ɓangaren ƙwaƙwalwa da kuma hankali, kuma hakan a nan gaba yana da tasiri akan kaifin hankalinshi, da wayonshi da yanayin fiskantarshi ababen da suke faruwa a rayuwa.

Haƙƙin yaro wajen saka mishi suna mai kyau

Kuma wannan ba wai haƙƙi ne na ganin dama ba, sai dai shi yana daga cikin ababen da suke wajibi akan uba, waɗanda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kwaɗaitar da sahabbanshi Allah Ya kara musu yarda akai; kaman yadda ya kasance yana umurtansu da nisantan sunaye masu munanan ma'ana, kuma himmatuwan Manzan Allah (S. A. W) akan kyawawan sunaye ya kai matsayin da ya canza sunayen wasu daga cikin sahabbanshi bayan shigansu Musulunci, domin abunda ke cikin haka na tasiri akan mutum da kuma dabi'unshi.

Hakkin yaro na yanka da raɗa suna

Shi ne abin da ake yanka wa jarirai –tare da keɓantattun niyya da kuma sharuɗɗa – domin nuna godiya ga Allah Ta’ala. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Kowane yaro yana jingine da ‘aqiqarsa ne, wadda za a yanka mishi a ranarshi ta bakwai, a aske gashin kanshi, kuma a sa mishi suna” (Abu Dawud 2838). Ya kuma ce: "Ga yaro na miji, tumaki biyu madaidaita, ga yarinya mace kuma, tunkiya guda" (Abu Dawud 2834).

Haƙƙin yara na mu'amala da adalci

Wannan ya shafi dukkanin ɓangarori, na zahiri da na ciki, ba tare da la'akari da jinsi ba. An karɓo daga Nu’uman Ɗan Bashir Allah Ya yarda da su ya ce: “Babana ya ba ni sadaka daga cikin dukiyarsa, sai mahaifiyata, Amrah Bintu Rawahah ta ce: Ba zan gamsu ba har sai ka sami shaidar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Sai mahaifina ya tafi wajen Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama ya shaida masa sadakar tawa. Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce masa: “Shin ka yi wa ƴaƴanka duka irin wannan kyautar?” Ya ce: A’a, Sai Annabi ya ce: “Kuji tsoron Allah, kuma ku yi adalci ga ƴaƴanku. Jin haka, sai mahaifina ya dawo ya janye wannan sadakar. (Al-Bukhari 2587, da Muslim 1623).

Haƙƙin yara na yi musu kyawawan Addu'a da nisantar yi musu munanan Addu'a

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Akwai addu’o’i guda uku da ake amsa su ba tare da shakka ba: Addu’ar wanda aka zalunta, da addu’ar matafiyi, da addu’ar iyaye ga ƴaƴansu” (Ibn Majah 3862). Kuma ya ce: "Kada ku yi wa kanku nummunar addu'a, kada ku yi wa ƴaƴanku mummunar addu'a, kuma kada ku yi wa dukiyoyinku mummunar addu'a, don kada ku dace da lokacin da ake roƙon Allah kyauta, sai ya amsa muku" (Muslim: 3009).

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa