Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Ma'anar Sallah da falalarta

Sallah tana da babban matsayi a cikin musulunci, kuma rukuni ce daga cikin manya-manyan rukunnanshi, kuma babban rukuni ne a cikin rayuwar musulmi. A cikin wannan darasin zaka san ma'anar sallah, da matsayinta da kuma falalarta.

  • Sanin Ma'anar Sallah
  • Sanin matsayin sallah a musulunci 
  • Sanin mahimmancin sallah da falalarta. 

Ma'anar Sallah

Ma'anan sallah a larabce: Shi ne Addu'a, kuma sallah ita ce sadarwa tsakanin bawa da Ubangijin shi Mahaliccinshi, domin ta ƙunshi mafi girman ma'anar bautan Allah da komawa zuwa gare Shi, da neman taimakonShi, sai mutum yayi addu'a ga Allah a cikinta, ya kuma gana da Shi, sai ranshi ya tsarkaka, kuma ya tuna haƙiƙaninshi da haƙiƙanin duniyar da yake rayuwa a cikinta, kuma yaji girman Allah Majiɓancin shi Mai yi mishi rahama, kuma a wannan lokacin ne sallarshi zata taimaka mishi wajen tabbata akan shari'ar Allah da kuma nisantar zalumci da alfasha da saɓo. Kamar yadda Allah Yace:(Lalle Sallah tana hanawa daga alfasha da kuma abun ƙi) (Al-Ankabut: 45).

Matsayin Sallah

Sallah ita ce mafi girman ibadar gangan jiki da kuma mafi darajansu, kuma ita ibadah ce wacce ta ƙunshi zuciya da hankali da kuma harce, mahimmancin sallah yana bayyana a cikin ababe masu yawa, daga cikinsu:

1- Lalle ita ce rukuni na biyu daga cikin rukunnan musulunci, kaman yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "An gina musulunci akan ababe guda biyar: Shaidawa babu abun bautawa da gaskiya sai Allah kuma Annabi Muhammadu Manzon Allah ne, da tsayar da Sallah..." (Bukhari: 8, Muslim: 16), kuma rukunin gini shi ne ginshiƙin da gini yake dogora akanshi kuma ba zai tsaya ba tare dashi ba.

2- Ita ce take bambanta tsakanin musulmai da kafurai, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Lalle abunda ke tsakanin mutum da shirka da kuma kafurci shi ne barin sallah" (Muslim: 82). Kuma yace: "Alƙawarin dake tsakanin mu da su shi ne sallah; kuma duk wanda ya barta haƙiƙa ya kafurta" (Attirmizi: 2621, Annasa'i: 463).

3. Allah Yayi umarni da a kiyaye ta a cikin dukkanin yanayi, a cikin tafiya da yayin da ake zaune, a cikin tashin hankali da kwanciyar hankali, a yanayin lafiya da rashin lafiya, kuma ana gudanar da ita ne gwargwadon iko, Allah Ta'ala Yace: (Ku kiyaye Salloli da kuma sallar tsakiya) (Albakara: 238), kuma Ya wasafta bayinShi muminai da faɗinShi:(Waɗanda suke kiyaye sallolinsu) (Muminun: 9).

Falalar Sallah

Dalilai da dama sunzo akan falalar sallah acikin littafin Allah da kuma sunnar AnnabinShi, daga cikinsu:

1- Tana kankare zunubi, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Salloli lokuta biyar, da jumma'a zuwa jumma'a, da Ramadan zuwa Ramadan, ana kankare zunuban da suke tsakaninsu idan aka nisanci manyan zunubai" (Muslim: 233, Attirmizi: 214).

2- Lalle ita haske ne mai haskakawa ga musulmi a cikin rayuwarshi baki ɗaya zatana karkatar da shi zuwa aikata alheri, ta kuma nisantar dashi daga sharri, Allah Ta'ala Yace: (Lalle Sallah tana hanawa daga alfasha da kuma abun ƙi) (Al-Ankabut: 45), Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace "Sallah haske ne" (Muslim: 223).

3- Ita ce farkon abunda za a yiwa mutum hisabi akai ranan alkiyama; idan ta inganta ta kuma karɓu, sauran dukkanin ayyuka sun karɓu, idan kuma bata inganta ba to za a dawar da dukkanin sauran ayyuka, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Farkon abunda za a fara yiwa mutum hisabi akai ranan alkiyama shi ne sallah, idan ta inganta dukkanin sauran ayyuka sun inganta" (Almu'ajam Al-Awsaɗ na Ɗabarani: 1859).

Lokacin Sallah shi ne lokaci mafi daɗi a wurin mumini domin a wannan lokacin ne yake ganawa da Ubangijin shi, sai ya samu kwanciyan hankali da natsuwa, da jin daɗin kasancewan shi tare da Allah Maɗaukakin Sarki.

Kuma ita ce mafificin abunda Annabi yake samun natsuwa da ita kaman yadda yace: "Kuma an sanya sanyin idanu na a cikin Sallah" (Annisa'i: 3940).

Sallah ita ce hutun Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana gayawa ladaninshi cewa: "Ya bilal ka tayar da Sallah, ka hutar damu da ita" (Abu Dawood: 4985).

Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan wani abu ya shigar da shi cikin baƙin ciki ko ya shagaltar da shi, sai yayi gaggawa zuwa Sallah (Abu Dawood: 1319).

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa