Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Siffar Sallah

Babu shakka lalle shari'a ta bayyana ingantacciyar hanyar gudanar da sallah domin ta zamto karɓaɓɓiya a wurin Allah Mai girma da ɗaukaka. A cikin wannan darasin zaka san siffar sallah da kuma yadda ake yinta.

Sanin siffar sallah

1- Anniyyah

Niyyah sharaɗi ne na ingancin sallah, abun nufi mai sallah yayi nufin bauta wa Allah da sallan a cikin zuciyarshi kuma yana sane da cewa lalle wannan sallar ta magariba ne alal misali ko ta isha ne, kuma ba a shar'anta yin furuci da wannan niyyar ba sai dai nufi da zuciya da kuma hankali shi ne abun buƙata, kuma furuta hakan kuskure ne; domin bai zo daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ko daga sahabbanshi masu girma ba.

2- Kabbara

Mai sallah zai tsaya yayin fara sallah sai yace: Allahu Akbar (Allah Shi ne mafi girma) sai ya ɗaga tafin hannayenshi zuwa kafaɗunshi ko kuma zuwa daura da kunnuwanshi, yana mai miƙe yatsunshi mai sanya tafin hannunshi suna fiskantar alkiblah.

Ma'anar kabbara

Kuma kabbara ba ta inganta sai da wannan lafazin (Allahu Akbar) kuma ma'anarta shi ne girmama Allah da kuma jinjina a gare Shi, domin Allah yafi kowa girma, yafi duniya girma da dukkanin ababen da suke cikinta na daga sha'awa da morewa, saboda haka mu jefar da dukkanin waɗannan ababen a gefe mu kuma fiskanci Allah Mai girma da ɗaukaka cikin sallah da zukatanmu, da hankulanmu muna masu ƙasƙantar da kai zuwa gare Shi.

3- Bayan kabbara sai ya sanya hannunshi na dama akan na hagu a bisa ƙirjinshi, kuma zai aikata hakan a koda yaushe yayin da yake tsaye.

4- Zai buɗe sallarshi da abunda ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na daga Addu'o'in buɗe sallah, kuma daga cikinsu akwai: "Subhanakallahumma wa bihamdika, tabarakas muka, wa ta'ala jadduka, wa la'ilaha gairuka".

5- Sai yace: (A'uzu billahi minash shaiɗanir rajim) wannan shi ne neman tsari daga Shaiɗan, ma'anarshi kuma shi ne: ina komawa zuwa ga Allah kuma ina neman tsarinShi daga Shaiɗan.

6- Sai yace: (Bismillahir Rahmanir Rahim), ma'anar basmalah kuma shi ne: Ina farawa da neman taimakon Allah ina mai neman albarkacin sunanShi.

Ya wajaba akan kowana musulmi da ya haddace suratul Fatiha; domin karanta ta rukuni ne a cikin sallah ga wanda yake sallah shi kaɗai ko ya kasance mamu a cikin sallar da liman baya bayyana karatu a cikinta.

7- Sai ya karanta suratul Fatiha, Fatiha kuma ita ce surah mafi girma a cikin littafin Allah, kuma haƙiƙa Allah Ya yiwa Annabi falala da sauƙar mishi ita, Allah Ta'ala Yace: (Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma) (Alhijir: 87). Bakwai abun maimatawa ita ce fatiha, kuma an saka mata wannan sunan ne domin ayoyinta guda bakwai ne, kuma ana maimaita ta sau da yawa a cikin Sallah a cikin kowace rana.

Ya wajaba akan kowana musulmi da ya haddace suratul Fatiha; domin karanta ta rukuni ne a cikin sallah ga wanda yake sallah shi kaɗai ko ya kasance mamu a cikin sallar da liman baya bayyana karatu a cikinta.

Suratul Fatiha

8- An shar'antawa mai sallah bayan karanta Fatiha ko sauraronta daga karatun limam da yace: (Ameen), ma'anarta kuma shi ne: Ya Allah Ka amsa mana.

9- Bayan karatun fatiha zai karanta wata surah a cikin raka'a ta farko da ta biyu, ko wasu ayoyi daga cikin wata surah, amma kuma raka'a ta uku da ta huɗu ana taƙaituwa ne a cikinsu da karanta suratul Fatiha.

Kuma karatun fatiha da abunda ke bayanta tana kasancewa ne a bayyane a cikin sallar asubahi da kuma raka'a ta farko da ta biyu na daga sallar magariba da isha, kuma tana kasancewa a asirce a cikin azahar da la'asar, da kuma a cikin raka'ah ta uku na daga sallar magariba da kuma raka'aa ta uku da ta huɗu na daga sallar isha.

10- Sa'annan yayi kabbara domin tafiya zuwa ruku'u yana mai ɗaga hannayenshi zuwa kafaɗunshi ko sama da su, yana mai sanya cikin tafukan hannunshi suna fiskantar alkiblah kamar yadda yayi a kabbarar farko.

11- Sai yayi ruku'u; Da sunkuyar da bayanshi ta bangaren alkiblah kuma sai ya daidaita bayanshi da kanshi, yana mai sanya tafukan hannunshi akan gwiwowinshi, kuma ya rarraba tsakanin yatsunshi, sai kuma yace: (Subhana rabbiyal Azim) kuma anso da ya maimaita wannan tasbihin har sau uku, amma kuma abunda yake wajibi shi ne sau ɗaya kawai, kuma ruku'u wajen girmama Allah ne da kuma jinjina miShi.

Ma'anar (Subhana rabbiyal azim) shi ne: Ina tsarkake Allah Mai girma kuma ina mai kore miShi dukkanin tawaya. Mai sallah zai faɗeta ne alhali yana cikin ruku'u.

12- Zai ɗago daga ruku'u zuwa yanayin tsayuwa yana mai ɗaga hannayenshi zuwa kafaɗunshi, cikin tafukan hannunshi kuma suna fiskantar alkiblah kamar yadda ya gabata, yana mai cewa: (Sami'allahu liman hamidahu) - Idan ya kasance shi ne liman ko yana sallah shi kaɗai- sai jama'a kuma suce: (Rabbana wa lakal hamdu).

Kuma anso da yayi ƙari sai yace bayanta: (Hamdan kasiran ɗayyiban mubarakan fihi, mil'as sama'i wa mil'al ardi, wa mil'a ma shi'ita min shai'in ba'adu).

13. Daga nan sai ya zube a ƙasa yana mai kabbara kuma mai sujjada a bisa gaɓɓanshi guda bakwai, kuma su ne: Goshi tare da hanci, da hannaye biyu, da gwiwowi biyu, da diga-digai biyu, kuma anso da ya nisantar da hannayenshi daga jikinshi, kuma ya nisantar da cikinshi daga cinyoyinshi, kuma ya nisantar da cinyoyinshi daga ƙafafunshi a cikin sujjadarshi, kuma ya raba zira'inshi da kasa.

14. Kuma zaice a cikin sujjadarshi: (Subhana Rabbiyal A'ala) sau ɗaya a bisa wajabci, kuma anso da ya maimaita ta har sau uku, kuma ma'anar (Subhana Rabbiyal A'ala) shi ne: Ina tsarkake Allah Maɗaukaki a cikin girmanShi da ikonShi Wanda Ya ɗaukaka a bisa sammanShi daga dukkanin tawaya da aibu, kuma a cikinta akwai faɗakar da mai sujjada wanda ke liƙe da ƙasa don ƙasƙastar da kai da tawali'u, akan banbancin dake tsakaninshi da Mahaliccinshi Mai girma, sai ya koma zuwa ga Ubangijin shi ya kuma ƙanƙan da kai ga Abun bautashi.

Falalar Sujjada

Sujjada tana daga cikin mafi girman wurin addu'a ga Allah Mai girma da ɗaukaka, sai musulmi ya roƙi Allah abunda yake so na alherin duniya da lahira a cikinta bayan yin zikirin da yake wajibi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Mafi kusancin wurin da bawa yake kasancewa ga Allah shi ne a lokacin da yake sujjada, saboda haka ku yawaita Addu'a a cikinta" (Muslim: 482).

15. Sa'annan sai yace: (Allahu Akbar), sai ya zauna a tsakanin sujjada biyu, kuma anso mishi da ya zauna akan ƙafarshi ta hagu ya kuma tayar da ta dama, sai ya sanya hannayenshi a bisa farkon cinyoyinshi sama da gwiwowinshi.

Siffar zama a cikin sallah

Kuma dukkanin zaman sallah anso su kasance kamar wanda ya gabata, sai dai zaman tahiyar ƙarshe, domin anso a cikinta da ya kafa ƙafarshi ta dama amma kuma zai fitar da ta hagu ta ƙarƙashinta sai ya zauna a ƙasa akan ɗuwawunshi na hagu.

Ambaton Allah a tsakanin sujjada biyu

16. Zai ce yayin da yake zaune a tsakanin sujjada biyu: (Rabbigfir li) kuma anso da ya maimaita ta har sau uku.

17. Sa'annan sai yayi wata sujjada tamkar ta farkon.

18. Sa'annan sai ya taso daga sujjada ta biyu zuwa yanayin tsayuwa yana mai cewa: (Allahu Akbar).

19. Sai ya sallaci raka'ah ta biyu tamkar ta farko, ba wani banbanci

20. Bayan sujjadarshi ta biyu a cikin raka'a ta biyu zai zauna irin zaman tsakanin sujjada biyu domin karatun tahiyyah, kuma zaiyi nuni da manuniyarshi ta hannun dama zuwa ɓangaren alkiblah sai yace: (Attahiyatu lillahi wassalawatu waɗɗayyibat, Assalamu alaika ayyuhan nabiyyu wa rahmatullahi wa barkatuhu, Assalamu alaina wa ala ibadil Lahis Salahina, Ash hadu an la'ilaha illal lahu, Wa ash hadu anna muhammadan abduhu wa rasuluhu).

21. Idan sallah ta kasance raka'a biyu ce; kaman sallar asubahi, toh lalle zai zo da salatul Ibrahimiyyah, sa'annan sai yayi sallama, bayani akan haka zai zo nan gaba. Amma kuma idan sallar ta kasance mai raka'a uku ne, ko mai raka'a huɗu, to lalle zai tashi domin kammala sauran sallarshi, sai dai zai taƙaita da karanta suratul Fatiha kawai a cikin raka'a ta uku da ta huɗu.

22. Sa'annan a cikin raka'a ta ƙarshe bayan sujjada ta biyu zai zauna domin karatun tahiyyar ƙarshe, kuma siffar zaman shi ne ya zauna akan ɗuwawunshi na hagu yana mai kafa ƙafarshi ta dama sai ya fitar da ƙafarshi ta hagu daga ƙarƙashinta, sai ya faɗi abunda ya faɗa a cikin tahiyar farko, sa'annan sai ya karanta salatul Ibrahimiyyah wanda shi ne: «Allahumma salli ala muhammad, wa ala ali muhammad, kama sallaita ala Ibrahima wa ala ali Ibrahim innaka Hamidun Majid, wa barik ala muhammad wa ala ali muhammad kama barakta ala Ibrahim wa ala ali Ibrahim innaka Hamidun Majid».

Kuma anso yace bayan haka: (A'uzu billahi min azabi Jahannam, wa min azabil ƙabir, wa min fitnatil mahya wal mamãt, wa min fitnatil Masihid Dajjal), kuma sai yayi addu'a da abunda yakeso.

23. Sa'annan sai ya juya zuwa ɓangaren dama yana mai cewa: (Assalamu alaikum wa rahmatullah), sai ya sake juyawa zuwa ɓangaren hagu ya faɗi kwatankwacin abunda ya faɗa a ɓangaren dama, kuma da sallama ne musulmi zai kasance ya kammala sallarshi kamar yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Shiganta shi ne kabbara kuma fita daga gare ta shi ne sallama" (Abu Dawood: 618, Attirmizi: 3) Ma'ana: Lalle Sallah ana shiganta ne da kabbarar farko ana kuma fita daga gareta ne da salama.

24. Anaso bayan sallama daga sallar farillah da mutum yace:

١
Astagfirullah (Sau uku)
٢
(Allahumma Antas Salam, wa minkas Salam, tabarakta Ya Zal Jalali wal ikram)
٣
(Allahumma la mani'a lima A'aɗaita wala mu'uɗiya lima mana'ata, wala yanfa'u zaljaddi minkal jaddu).
٤
Sa'annan sai yace (Subhanallah) sau 33,(Alhamdu lillah) sau 33,(Allahu Akbar) sau 33
٥
Kuma sai ya cika ɗari da faɗinshi cewa :(La ilaha illal lahu wahdahu la sharika lahu, lahul mulku, wa lahul hamdu wa Huwa ala kulli shai'in Ƙadir).

Wanda bai haddace Suratul Fatiha da zikirin sallah ba me zai aikata?

Ya wajaba a gare shi da ya ƙoƙarta matiƙar ƙoƙari wajen ganin cewa ya haddace suratul Fatiha da yaren larabci domin lalle sallah bata inganta sai da ita, kuma ya wajaba a gare shi da yayi matiƙar ƙoƙari wajen haddace ambaton Allan da suke wajibi a cikin sallah, kuma su ne: Fatiha, da kabbara, da Subhana rabbiyal Azim, da sami'al Lahu liman hamidahu Rabbana lakal hamdu, da Subhana rabbiyal A'ala, da Rabbigfirli, da tahiyah, da salati a bisa Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da kuma Assalamu Alaikum wa rahmatullah.

Kuma har zuwa lokacin da zai haddace toh ya wajaba akanshi da ya dinga maimaita abunda ya sani na daga tasbihi da kabbara da hamdala yayin sallah, ko kuma yata karanta ayar da ya haddace ta yayin tsayuwa domin faɗin Allah Ta'ala: (Kuji tsoron Allah gwargwadon ikonku) (Attagabun: 16).

Amma kuma sabon musulunta

Ya kamata ya zamto mai matiƙan kwaɗayi -gwargwadon iko -akan sallah cikin jama'a domin ya inganta sallolinshi, kuma domin lalle liman zan ɗauki wani ɓangare daga cikin tawayewan mamu.

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa