Ɓangaren yanzu model
Darasi Ƙiran Sallah
Allah Ya shar'anta wa musulmai ƙiran sallah domin ƙiran mutane zuwa ga Sallah da kuma sanar dasu shigan lokacinta.
Kuma an shar'anta ikama domin sanar dasu lokacin shiga sallah da kuma fara ta.
Yaya aka shar'anta ƙiran sallah?
Musulmai sun kasance yayin da suka taho zuwa Madinah suna taruwa suna tsayar da sallah, kuma babu wanda yake kira daga cikinsu, wata rana sai suka tattauna akan haka, sai wasunsu sukace: Mu riƙi ƙararrawa kamar na Nasara, wasunsu kuma suka ce muyi amfani da ƙaho irin na yahudu, sai Umar yace: Shin ba zaku tura wani daga cikinku ya kira sallah ba? Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Ya Bilal ka tashi ka ƙira mana sallah") Bukhari: 604, Muslim: 377).
Hukuncin ƙiran Sallah da Iƙama
Ƙiran sallah da iƙama wajibi ne akan jama'a banda mutum ɗaya, amma kuma idan suka barsu da gangan sallar su ta inganta sai dai sun aikata abunda ba dai dai ba.
An shar'anta ƙiran sallah da ɗagaggen sauti kuma kyakkyawa domin mutane suji su taho zuwa ga Sallah.
Kuma ladani zai ƙara faɗin:(Assalatu khairun minan naum, Assalatu khairun minan naum) a cikin sallar Asuba, bayan faɗin: (Hayya alal falalh).
Nanatawa a bayan ladan
Kuma anso ga wanda yaji ƙiran sallah da ya nanata a bayan ladan, sai ya faɗi kwatankwacin abunda ladan yake faɗa, sai idan ladan yace: (Hayya alas salat) ko (Hayya alal falah) sai shi kuma yace: (La haula wala ƙuwwata illa billah). Sa'annan bayan an gama ƙiran sallan sai yace:(Allahumma Rabba hazihid da'awatut Tammah, wassalatul ƙa'imah, Ãti muhammadan alwasilata walfadilah, wab'ashu maƙaman mahmudan allazi wa'adtah).