Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Sallar Jumma'a

Sallar jumma'a tana daga cikin sallolin farilla masu mahimmanci akan musulmai. A cikin wannan darasin zaka san falalar sallar jumma'a da hukunce-hukuncen ta.

Sanin falalar sallar jumma'a. Sanin siffar sallar jumma'a da hukunce-hukuncen ta. Sanin wanda za a mishi uzuri idan bai samu damar zuwa sallar jumma'a ba.

Sallar jumma'a

Allah Ya farlanta wata sallah a ranar jumma'a a lokacin sallan azahar, kuma tana daga cikin manya-manyan ibadu a musulunci, Ya kuma tabbatar da wajabcinta, musulmai suna taruwa sau ɗaya a cikin sati, su saurari wa'azi da faɗakarwa waɗanda limamin jumma'a zai gabatar musu, sa'annan sai su sallaci sallar jumma'a.

Falalan ranar jumma'a

Ranar jumma'a ita ce mafificiyar ranuka wacce tafi kowanne darajah, haƙiƙa Allah Ta'ala Ya zaɓe ta a bisa sauran ranaku, Ya kuma fifita ta akan sauran lokuta da ababe masu yawa, daga cikinsu:

1- Lalle Allah Ya keɓance Al-ummar Annabi da ita koma bayan wasunsu daga cikin Al-ummu, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: Allah Ya ɓatar da waɗanda suka rigaye mu akan jumma'a, sai yahudawa suka kasance suna da ranar asabar, nasara kuma suka kasance suna da ranar lahadi, sai Allah Yazo damu daga baya, sai kuma Ya shiryar damu zuwa ga ranar jumma'a" (Muslim: 856).

2. Lalle Annabi Adam alaihis salam an halicce shi ne ranar jumma'a, kuma alkiyama zata tsaya ne a ranar jumma'a, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Mafi alherin yinin da rana ta fito a cikinshi shi ne ranar jumma'a, a cikinta ne aka halicci Annabi Adam, a cikinta aka shigar da shi Aljannah, a cikinta aka fitar da shi daga gare ta, kuma alkiyama ba zata tashi ba sai a ranar jumma'a" (Muslim: 856).

Akan waye jumma'a take wajaba?

١
Na miji: Jumma'a bata wajaba akan ta mace ba.
٢
Mukallafi: Jumma'a bata wajaba akan mahaukaci, ko yaro ƙarami wanda bai balaga ba.
٣
Mazauni: Jumma'a bata wajaba akan matafiyi ko wanda yake zaune a jeji nesa da garuruwa da kuma birane.

Siffar sallar jumma'a da hukunce-hukuncen ta

Shiryawa sallar jumma'a

Anaso musulmi yayi wanka gabanin lokacin sallar jumma'a, da sammako zuwa masallaci kafin a fara huɗuba, da fesa turare, da sanya kyawawan tufafi.

Huɗubar Jumma'a

Musulmai suna taruwa a masallacin jumma'a, sai liman ya gabace su, ya hau kan Mimbari, yana mai fiskantar musulmai, sai yayi musu huɗuba guda biyu, yana mai raba tsakaninsu da ƙaramar zama, yana tunatar da su da tsoron Allah a cikinsu, kuma yana gabatar musu da nasihohi, da wa'azi yana kuma karanta musu ayoyi.

Ya wajaba akan musulmai da su saurari huɗuba, kuma magana ko shagaltuwa da wani abu yayin huɗuba ya haramta domin zai hana su amfanuwa da huɗubar, koda ace kuwa wasa da sallaya ne ko tsakuwa ko yashi ba aso.

Sa'annan sai liman ya sauƙo daga mimbari, sai a tayar da sallah, sai ya yiwa mutane sallah raka'a biyu yana mai bayyana karatu a cikinsu.

Wanda sallar jumma'a ta wuce shi

An shar'anta sallar jumma'a ne da taruwan musulmai a cikin masallaci, saboda haka duk wanda jumma'a ta wuce shi ko bai samu zuwa ba saboda uzuri, toh lalle zaiyi sallan azahar ne a madadin ta, kuma jumma'a ba zata inganta daga gare shi ba.

Wanda yayi jinkirin zuwa sallar jumma'a

Duk wanda yayi jinkirin zuwa sallar jumma'a kuma ya riski ƙasa da raka'a ɗaya tare da liman, to lalle shi zai cika sallan azahar ne.

Duk wanda sallar jumma'a bata wajaba akanshi ba kaman mace da matafiyi, to lalle jumma'a tana inganta daga garesu idan suka sallace ta tare da jama'an musulmai, sai sallan azahar kuma ta faɗi daga gare su sakamakon sallan jumma'ar da sukayi tare da jama'an musulmai.

Wajabcin halartan jumma'a

Shari'a ta tabbatar da wajabcin halartan jumma'a ga waɗanda take wajibi akansu, kuma tayi gargaɗi akan barinta ta hanyar shagaltuwa da ƙele-ƙelen duniya, Allah Ta'ala Yace: (Ya ku waɗanda sukayi imani, idan aka ƙira sallah a ranar jumma'a to kuyi gaggawa zuwa ambaton Allah kuma ku bar kasuwanci, wannan shi ne mafi alheri a gare ku da kun kasance kun sani)(Aljuma'a: 9).

Da menene Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya tsoratar da waɗanda suke saɓa zuwa sallar jumma'a?

Annabi ya tsoratar da waɗanda ba sa zuwa sallar jumma'a ba tare da uzuri ba da cewa Allah Zai toshe zukatansu, Manzon Allah yace: "Duk wanda ya bar sallar jumma'a guda uku domin wulaƙanta ta ba tare da wani uzuri ba Allah zai toshe zuciyarshi" (Abu Dawood 1052, Ahmad: 15498), Ma'anan Allah Zai toshe zuciyarshi shi ne Allah zai rufe ta Ya kuma sanya jahilci da jafa'i a cikinta sai ta zamto tamkar zukatan munafukai da masu saɓo.

Wana uzuri ne karɓaɓɓe wajen barin sallar jumma'a?

Karɓaɓɓen uzurin barin sallar jumma'a ga wanda ta wajaba a gare shi shi ne: Duk wani abunda zai haifar da wata wahala mai tsanani wacce ba a saba da ita ba, ko ake tsoron cutarwa daga gare ta, wacce zata iya cutar da rayuwar musulmi ko lafiyarshi.

Shin kasancewa a wurin aiki uzuri ne na barin sallar jumma'a?

Kasancewa a wurin aiki koda yaushe ba uzurin barin sallar jumma'a bane ga wanda take wajibi akanshi sai dai a cikin yanayi biyu:

1. Ya kasance a wurin aikin akwai wata maslaha babba wacce ba za a cimma ta ba sai ya kasance yana wurin, kuma barin wurin zai iya haifar da babban ɓarna, kuma babu wani wanda zai iya maye gurbinshi a cikin wannan aikin.

Misalai

١
Likitan dake ɗakin kula da marasa lafiyan waɗanda suke buƙatan kulawa na gaggawa.
٢
Mai gadi da kuma jami'in tsaro waɗanda suke kula da dukiyar mutane, kuma suke kare ta daga sace ta ko lalata ta.
٣
Wanda yake saka ido akan ingancin manya-manyan kamfanoni da makamantansu, waɗanda dole sai an maida hankali akansu a kowana lokaci kuma ba za a iya tsayar da su ba.

2. Wanda wannan aikin ya kasance daga shi ne kawai yake samun arzikinshi, kuma bayi da wata hanyar da zai biya buƙatunshi da suka zamto wajibi na daga abinci, da abun sha, da ababen da suka zamto dole a gare shi da kuma iyalanshi, to ya halatta a gare shi da ya zauna a wurin aikin tare da barin sallar jumma'a a bisa larura har sai ya samu wani aiki na daban, ko ya samu abunda zai wadatar dashi na daga abinci da abun sha da ababen da suka zamto wajibi a gare shi da iyalanshi, kuma duk da hakan, ya wajaba a gare shi da ya kasance yana neman wani aiki daban ko wata hanyar samun kuɗi ta daban.

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa