Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Zakkah: Haƙiƙaninta Da Manufofinta

Zakkah ita ce rukuni na uku daga cikin rukunnan musulunci. A cikin wannan darasin zaka san haƙiƙaninta da manufofinta, da kuma hikimar shar'anta ta.

  • Sanin haƙiƙanin Zakkah. 
  • Sanin Manufar shar'anta ta. 
  • Sanin waɗanda za a baiwa Zakkah. 

Zakkah

Zakkah ita ce rukuni na uku daga cikin rukunnan musulunci, kuma ita wajibi ne na dukiya wanda Allah Ya farlanta wa masu kuɗi domin su baiwa talakawa da mabuƙata da wasunsu na daga waɗanda suka cancanci wani kashi na musamman daga dukiyarsu domin magance matsalolinsu.

Manufofin Zakkah

1. Lalle an halicci rai da son dukiya, wanda hakan ya saka mutum yake kwaɗaituwa wajen ganin ya kiyaye ta kuma yayi riƙo da ita, sai Allah Ya shar'anta fitar da Zakkah domin tsarkake rai daga cutar rowa da kwaɗayi, da kuma magance son duniya da riƙo da ƙawarta, Allah Ta'ala Yace: (Ka ɗauka daga cikin dukiyarsu sadaka ce, zaka tsarkake su kuma zaka tsaftace su da shi)(Attaubah: 103).

2. Fitar da zakkah yana ƙarfafa igiyar soyayya da tausayawa; saboda Allah Ya halicci ran mutum akan son wanda ya kyautata mata, da hakane mutane zasu rayu tare cikin soyayya da haɗin kai, tamkar tabbataccen gini wani shashi yana ƙarfafa wani shashin, kuma sai cutar sata, da fashi da yaudara su ragu a cikin Al-ummah.

3. Da fitar da zakkah ne za a tabbatar da ma'anar bauta wa Allah da ƙasƙantar da kai zuwa gare Shi, da kuma cikakken miƙa wuya ga Allah ubangijin talikai, domin a yayin da mawadaci ya bayar da zakkan dukiyarshi zai kasance ya aiwatar da shari'ar Allah ya kuma zantar da umarninShi, kuma a cikin fitar da zakkah akwai godewa ni'imar Allah Mai girma da ɗaukaka, kuma Allah zai saka mishi a bisa wannan godiyar, Allah Ta'ala Yace: (Lalle idan kuka gode zan ƙara muku) (Ibrahim: 7).

4. Za a samu haɗin kai sosai da kuma fahimtar juna cikin bayar da zakkah, kuma za a samu wani nau'i na daidaito tsakanin mutanen dake rayuwa a wuri guda, domin da bayar da ita zuwa waɗanda suka cancance ta ne dukiya ba zata zamto a koda yaushe tana daskare a hannun mawadata ba. Allah Ta'ala Yace: (Domin kada dukiyar ta zamto tana jujjuyawa a tsakanin mawadata daga cikinku) (Alhashr: 7).

Waye za a baiwa Zakkah?

Musulunci ya ƙayyada kalan mutanen da za a baiwa zakkah. kuma ya halatta ga mutum da ya baiwa kala ɗaya daga cikinsu ko kuma fiye da haka, ko ya baiwa ma'aikata da hukumomin ayyukan alheri waɗanda suke ɗaukan nauyin raba ta ga waɗanda suka cancance ta na daga cikin musulmai, amma kuma abunda yafi shi ne a rabata a cikin garin da wanda ya fitar da zakkan yake rayuwa.

Nau'in Mutanen da za a baiwa zakkah:

١
Talakawa: Kalmar talakawa Jam'i ne na talaka, kuma shi ne wanda bai da komai gaba ɗaya, ko kuma yana samun ƙasa da rabin abunda zai ishe shi a shekara.
٢
Miskinai: Jam'in miskini, kuma shi ne wanda yake samun rabin abunda zai ishe shi ko fiye da haka a cikin shekara.
٣
Masu aiki akanta: Su ne ma'aikata da kuma waɗanda shugaba yake amfani dasu wajen tara zakkah da kuma raba ta.
٤
Waɗanda ake rarrashin zukatansu: Su ne shuwagabannin da ake musu biyayya a cikin mutanensu, domin tsammanin musuluntarsu, ko musuluntar mutanensu, ko ƙarfafa imaninsu, ko kare su daga musulmai idan ana jin tsoron sharrinsu.
٥
Da waɗanda suke cikin bauta: Abun nufi dasu shi ne waɗanda sukayi yarjejeniya da shuwagabannin su mamallakansu akan cewa zasu basu wani kuɗi domim su zamto ƴaƴa ba bayi ba, kuma za a iya sayan bawa da zakkah, ko kuma a ƴanto bayi musulmai da ita.
٦
Da waɗanda ake bi ba shi: kuma su ne waɗanda suka ciwa kansu bashi -da sharaɗin cewa sun ci bashin ne don aikata abunda ke halal- sa'annan sai suka gaza biyan ba shin, ko kuma waɗanda suka ci ba shi domin kwantar da tarzoma.
٧
Da waɗanda suke tafarkin Allah: Abun nufi su ne mayaƙa waɗanda suka ba da kansu ga jihadi don ba da kariya ga musulunci, kuma babu wani sakamako na kuɗi da ake basu ko salari daga cikin dukiyar musulmai.
٨
Da wanda yake kan hanya: Shi ne matafiyi wanda guzurinsa ya ƙare a garin da ba nashi ba, sai a ba shi abunda zai isar da shi garin da ya dosa, da sharaɗin kada wannan tafiyar ta kasance ta haramun ne.

Allah Maɗaukakin Sarki Yace Yana Mai bayyana nau'in waɗanda za a baiwa zakkah:(Abin sani kawai shi ne, lalle dũkiyõyin sadaka na faƙĩrai ne da miskinai da mãsu aiki a kansu, da waɗanda ake lallãshin zukãtansu, kuma a cikin fansar wuyõyi, da waɗanda ake bi bashi, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla ce daga Allah. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima) (Attaubah: 60).

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa