Ɓangaren yanzu model
Darasi Dukiyoyin da zakkah suka wajaba a cikinsu
Su waɗanne dukiyoyin ne zakkah ta wajaba a cikinsu?
Zakkah bata wajaba a cikin abunda musulmi ya mallaka wanda yake amfani da shi da kanshi kaman gidanshi da yake zaune a ciki ko yaya tsadanshi ya kasance, ko motarshi da yake amfani da ita koda ace mai tsada ce sosai, hakama tufafinshi da abin cinshi da abun shan shi.
Allah Ya wajabta zakkah a cikin wasu nau'i na dukiya waɗanda suke da yanayin ƙaruwa, kuma su ne:
Kuma Zakkah bata wajaba akansu har sai sun kai nisabin shari'a, kuma sun kai shekara cikakkiya, wato tsawon kwanaki 354.
Nisabin Zakkah a cikin zinari da azurfa shi ne kaman haka:
Idan musulmi ya kasance ya mallaki wannan adadin -ko fiye da haka- na daga zinari ko azurfa, sa'annan suka kai shekara a wajenshi, to babu shakka zai cire musu zakkan da ya kai kimanin 2.5% daga kimarsu.
Dukiya ta haɗa da takardun kuɗaɗe daban-daban koda ace suna hannunshi ne ko ya ajiye su a banki
Musulmi zai lissafa nisabin dukiyarshi da kuɗaɗenshi ne da abunda zai kasance dai-dai da kimansu na daga zinari, idan ya kasance yana da dukiyar da takai nisabin zinari, wato kaman kimanin giram 85, ko fiye da hakan a lokacin da zakkah ta wajaba, kuma wannan dukiyar ta zauna a wajenshi har na tsawon shekara guda, to zai cire 2.5% na daga kimarta.
Misali akan nisabin zakkan dukiya:
Da za ace alal misali farashin giram na zinari a yayin da zakkah ta wajaba ya kai kimanin dala 25, to nisabin zakkan dukiya zai zamto kaman haka: 25 (farashin giram ɗin zinari, kuma shi abune mai canzawa) × 85 (Adadin giram ɗin, abu ne ba mai canzawa) = dala 2125.
Abun nufi da hakan shi ne: Duk wasu ababen da aka tanade su don kasuwanci kaman filaye da gine-gine, da shaguna da gidaje, ko kuma ababen abincin da ake amfani dasu yau da kullum
Yadda ake fitar da zakkan ababen kasuwanci
Mutum zai ɗauki ƙimar dukkanin ababen da ya sanya su a cikin kasuwancin idan shekara ta kewayo, sai ya ƙimanta su da farahin wannan ranan da yaso ya cire zakkan a cikinsu, idan har wannan kiman ya kai nisabin zakkan dukiya sai ya cire kimanin 2.5% daga kimarsu.
Allah Maɗaukaki Yace: (Ya ku waɗanda sukayi imani ku fitar daga ababe kyawawan da kuka samu da kuma ababen da Muka fitar muku da su daga cikin ƙasa) (Albakara: 267).
Zakkah tana wajaba a cikin wasu nau'uka na musamman na daga amfanin gona, ba wai a cikin dukaninsu bane, kuma su ma dole ne sai sun kai wani nisabin da shari'a ta tanada.
Kuma ana bambanta tsakanin wanda aka shayar da shi da ruwan sama da wanda aka shayar da shi da ƙoramai da kuma wanda aka shayar dashi da wahala da biyan kuɗaɗe wajen nisabin da ya wajaba a fitarwa zakkah domin la'akari da yanayin mutane.
Sharruɗan wajabcin zakkan hatsi da ƴaƴan itatuwa
1. Sai abunda aka samu ya kai nisabi
Kuma lalle Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bayyana nisabin da zakkah yake wajaba a cikinshi, kuma zakkah bata wajaba a cikin abunda yake ƙasa da hakan, sai yace: "Babu zakkah a ƙasa da buhu biyar na dabino" (Bukhari: 1459, Muslim: 980). Kuma shi ne kimanin kilo amma saidai shi ana ƙaddara shi ne da mizani na daga alkama da shinkafa mai nauyi da kimanin 612 kilo giram, kuma babu zakkah a cikin ƙasa da hakan.
2. Kuma abunda aka shukan sai ya kasance cikin nau'ukan da zakkah ta wajaba a kansu
Kuma zakkah bata wajaba sai a cikin amfanin da za a iya adanawa da kuma ajiyewa ba tare da ya ɓaci ba kaman alkama da shinkafa, da dabino da gero da makamantansu, amma kuma kayan marmari da ganyaye waɗanda ba za a iya adana su ba zakkah bata wajaba a cikinsu, kaman su kankana da rumman da tumaturi da dankalin turawa da makamantansu.
3. Ya zamto an kammala girbe shi
Zakkah tana wajaba ne akan amfanin da aka gama girbe su, kuma zakkan amfanin gona bai da alaƙa da wucewan shekara, idan amfanin ya kasance ana girbewa sau biyu ne a shekara, to zakkah zata wajaba ne a duk lokacin da aka girbe shi, kuma idan ya cire mishi zakkan sai ya ajjiye shi na tsawon shekaru, toh babu zakkah akanshi a cikin waɗannan shekarun.
Abun nufi da dukiyar dabbobi shi ne ababen da mutum yake amfani dasu na daga dabbobi, musamman ma: Raƙuma, Shanaye, tumakai.
Kuma hakika Allah Yayiwa bayinShi ni'ima da halittan wadannan dabbobin domin su ci daga namansu, kuma su sanya fatunsu, kuma su dinga ɗaukansu da kayakin nauyinsu yayin tafiya da balaguro, Allah Ta'ala Yace:(Da dabbõbin ni'ima, Ya halicce su dõminku. A cikinsu akwai abin yin ɗumi da waɗansu amfãnõni, kuma daga gare su kuke ci * Kuma kunã da kyau a cikinsu a lõkacin da suke kõmõwa daga kĩwo da maraice da lõkacin da suke sakuwã * Kuma sunã ɗaukar kãyanku mãsu nauyi zuwa ga wani gari, ba ku kasance mãsu isa gare shi ba, fãce da tsananin wahalar rãyuka, Lalle ne Ubangijinka ne, haƙĩƙa, Mai tausayi, Maijin ƙai)(Alnahl: 5 -7).