Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Azumin watan Ramadan

Azumin watan Ramadan shi ne rukuni na huɗu daga cikin rukunnan musulunci da kuma ginshiƙun shi masu ƙarfi. A cikin wannan darasin zaka san ma'anan azumi da kuma falalan watan Ramadan.

  • Sanin ma'anan azumi da falalarshi. 
  • Sanin falalar watan Ramadan 

Allah Ya farlantawa musulmai azumin wata guda a cikin shekara, kuma wannan watar ita ce watan Ramadan mai albarkah, kuma Ya sanya shi rukuni na huɗu ne daga cikin rukunnan musulunci da kuma ginshiƙun shi masu girma, Allah Ta'ala Yace: (Ya ku waɗanda sukayi imani an farlanta muku azumi kaman yadda aka farlantawa Waɗanda suka rigaye ku domin kuji tsoron Allah) (Albakara: 183).

Ma'anar Azumi

Ma'anar azumi a musulunci shi ne bautatawa Allah da kamewa da kuma barin ci da sha da jima'i da dukkanin sauran ababen da suke lalata azumi daga ketowan alfijir ɗin gaskiya -kuma shi ne lokacin shigan sallar asubahi - har zuwa faɗuwan rana, kuma shi ne lokacin shigan sallar Magariba.

Falalar watan Ramadan

Watan Ramadana shi ne wata na tara a cikin jerin watannin shekara a kalandar musulunci, kuma shi ne mafificin watannin shekara, wanda Allah Ya keɓance shi da dayawa na daga falala akan waninshi na daga watanni, daga cikin waɗannan falalan:

1. Shi ne watan da Allah Ya keɓance shi da sauƙar da mafi girman litattafai (Alkur'ani mai girma)

Allah Ta'ala Yace: (Watan Ramadan shi ne wanda aka sauƙar da Alkur'ani a cikinshi domin ya zamto shiriya ga mutane da kuma bayyana ababen shiriya da rarrabewa, saboda haka, duk wanda ya riski watan Ramadan a cikinku to ya azumce shi) (Albakara: 185).

2. Shi ne watan da ake buɗe ƙofofin Aljannah a cikinshi

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Idan watan Ramadan ya shiga sai a buɗe ƙofofin Aljannah, a kuma kulle ƙofofin Jahannama, kuma a ɗaure shaidanu" (Bukhari: 3277,Muslim: 1079). Haƙiƙa Allah Ya shiryawa bayinShi fiskantar wannan wata da aikata kyawawan ayyuka da kuma barin munanan ayyuka.

3. Duk wanda ya azumci yininshi ya kuma sallaci darenshi an gafarta mishi abunda ya gabatar na daga zunubanshi

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Duk wanda ya sallaci watan Ramadan yana mai imani da kuma neman lada, an gafarta mishi abunda ya gabatar na daga zunubanshi" (Bukhari: 2009,Muslim: 759).

4. A cikinshi akwai lailatul ƙadari, mafi girman daren shekara

Kuma shi ne daren da Allah Ya bada labari a cikin littafinShi cewa lalle aikin alheri a cikinshi yafi aiki a cikin watanni dubu. Allah Ta'ala Yace: Daren lailatul ƙadari yafi alheri fiye da watanni dubu) (Alkadar: 3), Kuma shi dare ne wanda ba a ayyana shi ba sai dai yana daga cikin goman ƙarshe na daga watan Ramadan, duk wanda ya sallace shi yana mai imani da kuma neman lada an gafarta mishi abunda ya gabatar na daga zunubanshi.

Falalar Azumi

Azumi yana da falala mai yawa waɗanda suka zo a cikin shari'ar musulunci, daga cikinsu:

1. Gafarta Zunubbai

Duk wanda ya azumci watan Ramadan yana mai imani da Allah mai bin umarninShi, yana kuma mai gaskata ababen da sukazo na daga falalanshi, yana mai neman lada a wurin Allah, an gafarta mishi abunda ya gabatar na daga zunubanshi, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Duk wanda ya azumci watan Ramadan yana mai imani da neman lada a wurin Allah, an gafarta mishi abunda ya gabatar na daga zunubanshi" (Bukhari: 2104, Muslim: 760).

2. Lalle mai azumi zaiyi farin ciki da abunda zai samu na daga sakamako da kuma ni'ima yayin saduwa da Allah

Kaman yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Mai azumi yana da farin ciki guda biyu: Farin ciki yayin buɗa bakinshi, da kuma farin ciki yayin saduwa da Ubangijinshi" (Bukhari: 1904,Muslim: 1151).

3. A cikin Aljannah Akwai wata ƙofar da ake cewa da ita Ar-Rayyan babu wanda zai shiga ta cikinta sai masu azumi.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Lalle a cikin Aljannah akwai wata ƙofa ana ƙiranta Ar-rayyan, masu azumi ne kaɗai zasu shiga ta cikinta a ranan alkiyama, kuma babu wani wanda zai shiga ta cikinta tare dasu, za ace: Ina masu azumi? sai su tashi, babu wani wanda zai shiga ta cikinta tare da su, idan suka gama shiga sai a kulleta ta yadda babu wanda zai sake shiga ta cikinta" (Bukhari: 1896, Muslim 1152).

4. Lalle Allah Ya danganta sakamakon azumi da ladanshi zuwa gare Shi

Kuma duk wanda ladanshi da sakamakon shi ya kasance a wurin Allah Mai girma, Mai karamci, Mai yawan kyauta, Mai yawan rahama ne, to lalle yayi farin ciki da abunda Allah Ya tanada mishi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace a cikin hadisin ƙudusi wanda ya rawaito shi daga Ubangijinshi: "Dukkanin ayyukan ɗan Adam nashi ne saidai azumi, domin lalle shi Nawa ne kuma Ni ne zan bayar da ladanshi" (Bukhari: 1904, Muslim: 1151).

Hikimar dake cikin Azumi

Allah Ya farlanta Azumi domin hikimomi masu yawa da amfani da dama a cikin addini da kuma duniya. daga cikinsu:

1. Samun tsoron Allah Mai girma da ɗaukaka

Domin azumi ibada ne wanda bawa yake samun kusanci zuwa ga Allah dashi, ta hanyan barin ababen da yakeso, da daƙile sha'awarshi wacce take halal, domin bin umarnin Ubangijinshi da kuma gujewa saɓa miShi.

2. Koyon barin aikin zunubi da saɓo

Domin ƙauracewa ababen da suke halal da mai azumi yayi domin bin umarnin Allah Ta'ala zai taimaka mishi wajen danne sha'awarshi ga barin aikin zunubi.

3. Tuna marasa wadata da taimaka musu

Domin lalle a cikin azumi akwai yanayin tunawa da marasa hali da kuma jin yunwa, wanda hakan zai sa a tuna da talakawa waɗanda suke fama da talauci a rayuwarsu, sai bawa ya tuna da ƴan uwanshi talakawa da yadda suka kasance suna wahala daga yunwa da kuwa ƙishirwa, sai yayi ƙoƙari wajen taimaka musu da kuma agaza musu.

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa