Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Eidi

Eidi yana daga cikin ibadun Allah waɗanda suke a bayyane, kuma lalle Allah Ya sanyawa kowana mutane ranakun Eidinsu waɗanda suka keɓanta dasu. A cikin wannan darasin zaka koya wasu ababen da suke da alaƙa da Eidi a cikin Musulunci.

  • Sanin Eidukan Musulmai. 
  • Sanin siffar yadda ake sallar Eidi. 
  • Sanin wasu hukunce-hukunce da ladduban da suke da alaƙa da Eidi. 

Eidi yana daga cikin alamun bautan Allah na zahiri

Yayin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya tafi zuwa Madinah sai ya samu Ansar -Musulman garin Madinah- suna wasa kuma suna murna a cikin ranaku biyu na daga shekara, sai yace: Wana ranaku ne waɗannan"? sai sukace: mun kasance muna wasa a cikinsu ne a cikin jahiliyyah, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Lalle Allah Ya sauya muku su da waɗanda suka fisu alheri: Ranar Laiha, da ranar sallar azumi" (Abu Dawood: 1134). kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace yana mai bayyana cewa lalle Eidi yana daga cikin ayyukan addini: "Lalle kowana mutane suna da Eidinsu, kuma wannan shi ne Eidinmu" (Bukhari: 952. Muslim: 892).

Eidi a cikin musulunci

Eidi a cikin musulunci shi ne Ranar da musulmai suke bayyana farin ciki a cikinshi domin kammala ibadah don nuna godiya ga Allah ta'ala a bisa shiriyarShi, da datarwarShi ga ibadah, kuma an shar'anta shigar da farin ciki cikin zukatan mutane gaba ɗaya a cikin ta, da sanya mafi kyawun tufafi, da kyautatawa mabuƙata, da hutar da rai da dukkanin ababen da suke halal kaman bukukuwa da shugulgula waɗanda suke shigar da murna cikin zukatan kowa da kowa, da kuma tunatar dasu ni'imar Allah akansu.

Musulmai suna da Eidi guda biyu waɗanda suke bukukuwa a cikinsu, kuma baya halatta da a keɓance wata ranan da mutane zasu dauke ta a matsayin ranar Eidi koma bayan ranaku biyun nan, kuma waɗannan ranakun su ne:

١
Eidin Sallar Azumi: Kuma shi ne ranan farko na daga watan shawwal
٢
Eidin sallar laiha: Kuma shi ne ranan goma na daga watan Zul-Hijjah

Sallar Eidi

Ita ce sallar da musulunci ya ƙarfafa ta ya kuma kwaɗaitar da musulmai maza, da mata ,da yara akan fita zuwa gareta. lokacinta shi ne daga ɗagowan rana daidai da mashi a sama bayan fitowarta a ranar Eidi har zuwa zawalinta (Ma'ana gusewanta daga tsakiyan sararin sama).

Siffar Sallan Eidi

Sallar Eidi raka'a biyu ne, Limami yana bayyana karatu a cikinsu, kuma zaiyi huɗuba guda biyu bayan sallah, kuma an shar'anta ƙara kabbarori a farkon kowace raka'ah a sallar Eidi, sai liman yayi kabbara guda shida gabanin fara karatu a raka'ar farko koma bayan kabbarar harama, kuma zaiyi kabbara biyar a raka'a ta biyu banda kabbarar tasowa daga sujjada.

An shar'anta yaɗa murna da farin ciki ga iyalai a ranar Eidi

Na daga yara, da manya, da maza, da mata da dukkanin hanyoyin da suke na halal, da sanya mafi kyawun tufafi, da kuma bautawa Allah da ci da sha a yini wannan ranar, saboda haka ne ma aka haramta azumtar ranar Eidi.

Kabbara a cikin ranakun Eidi biyu

An shar'anta kabbara a cikin ranar Eidin sallar azumi; domin bayyana farin ciki da ranar Eidin, da kuma kammala azumin ramadan mai albarkah, da kuma godewa ni'imar Allah akanmu a bisa shiryar damu da Yayi zuwa ga azumi, Allah Ta'ala Yace: (Domin ku cika lissafi kuma ku girmama Allah a bisa abunda Ya shiryar daku zuwa gare shi kuma domin ku gode) (Albakara: 185). Kuma an shar'anta kabbarori a cikin Eidin sallar laiha ma domin bayyana farin ciki, da gudanar da faralin hajji ga Alhazai, da kuma datarwa ga ayyukan alheri a cikin kwanaki goma na Zul-Hijjah ga Alhazan da kuma sauran musulmai, Allah Ta'ala Yace: yayin ambaton ababen da ake yankawa a laiha:(Namansu da jininsu basa riskan Allah sai dai tsoron Allanku ne yake riskanShi, kaman hakane muka horar muku dasu, domin ku girmama Allah a bisa abunda Ya shiryar daku, kuma ka yiwa masu kyautatawa albishir) (Alhajji: 37).

Yadda ake kabbarorin Eidi

Allahu Akbar Allahu Akbar, La ilaha illal lah, Allah Akbar Allahu Akbar wa lillahil hamdu. kuma sai yace: Allahu Akbar Kabiran, walhamdu lillahi kasiran, wa subhanallahi bukratan wa asila.

Kuma an shar'anta wa maza ɗaga muryansu ta yadda ba za su cutar da mutane ko su takura musu ba, mata kuma zasu sauƙe sautinsu da su.

Ka saurari kabbarorin Eidi daga Masallacin Harami a Makkah Almukarramah

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa