Ɓangaren yanzu model
Darasi Eidin sallar azumi da Eidin sallan Laiha
Eidin Sallan Azumi
Shi ne ran ɗaya ga watan shawwal; Wata na goma a jerin kalandar musulunci, kuma yana zuwa ne bayan ƙarewan ranar ƙarshe na daga watan Ramadan, saboda hakane ake ƙiranshi Eidul fiɗir (Eidin buɗa baki), saboda mutane suna bautawa Allah da cin abinci a cikin wannan rana kamar yadda suka bauta mishi da azumi a cikin watan Ramadan, su suna murna da eidin ne domin godiya zuwa ga Allah a bisa kamalar ni'imarShi da falalarShi da Ya yassare musu kammala azumin ramadan mai albarkah, Allah Ta'ala Yace:(Kuma domin ku cika lissafi kuma ku girmama Allah a bisa abunda ya shiryar daku zuwa gare shi kuma domin kuyi godiya) (Albakara: 185).
Menene aka shar'anta a ranar Eidin sallan Azumi?
Allah Ya farlantawa duk wanda ya mallaki sama da abunda yake buƙata na daga abinci a ranar eidi da darenta da ya fitar da kimanin mudu ɗaya na daga abincin mutanen garin na daga alkama ko shinkafa, ko masara, ko dabino ya baiwa talakawa da miskinai na daga cikin musulmai, domin kada a samu wani mabuƙaci a ranar Eidi.
Daga faɗuwan ranar ranan ƙarshe na daga watan Ramadan har zuwa lokacin sallan Eidi, kuma ya halatta da a gabatar da ita kafin ranar Eidi da kwanaki biyu ko da kwana ɗaya.
Mudu ɗaya na daga abincin mutanen garin na daga alkama ko shinkafa ko masara ko dabino da makamantanau, Mudu kuma shi ne kwatankwacin kilo guda, amma kuma ƙaddara shi da ma'auni yafi domin gane asalin kimarshi, kuma shi ne kaman kimanin nauyin kilo giram 3
Tana wajaba ne akan wanda ya mallaki fiye da abunda yake buƙata na daga abinci wanda zai wadatar da shi da kuma waɗanda suke ƙarkashin shi kaman matarshi da yaranshi a ranar eidi ko a daren shi, kuma anso da a fitarwa jinjirin dake cikin mahaifiyarshi, sai a fitarwa kowana mutum mudu guda na daga abincin mutanen garin, wato kilo giram 3 a taƙaice.
Hikimar dake cikin fitar da zakkan fidda kai
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya farlanta ta ne domin ta tsarkake mai azumi daga wasa da kuma wargi (Ma'ana domin tsarkake mai azumi daga kura-kurai da zamiya, don kuma ta cika mishi tawayar da akan iya samu a cikin azuminshi).
Kuma shi ne Eidi na biyu ga musulmai, yana kuma zuwa ne a ranar goma ga watan Zul Hijjah (Wata ta goma sha biyu a cikin jerin kalandar musulunci), kuma lalle an tara falala masu yawa a cikinshi, daga cikinsu:
1. Yana daga cikin mafifitan kwanakin shekara
Domin mafifitan kwanakin shekara su ne farkon kwanaki goma na daga watar Zul Hijjah, kaman yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Babu wasu kwanakin da ayyukan alheri sukafi soyuwa zuwa ga Allah kaman waɗannan kwanaki goman», sai sukace: Ya Manzon Allah, har da jihadi a tafarkin Allah? sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Har da jihadi a tafarkin Allah, sai dai mutumin da ya fita da kanshi da kuma dukiyarshi sa'annan bai dawo da komai daga wannan ba» (Bukhari: 969,Attirmizi: 757).
A cikinshi ne ake aiwatar da manya-manyan ayyukan hajji da waɗanda sukafi kowanne mahimmanci da darajah, kaman ɗawafi a kewayen Ka'abah, da yanka hadaya,, da jifan Shaiɗan.
Menene aka shar'anta a cikin ranar Eidin laiha?
An shar'antawa waɗanda ba Alhazai ba a cikin ranar Eidin laiha dukkanin ababen da aka shar'anta a ranan Eidin sallan Azumi mai albarkah sai dai zakkan fidda kai domin ita ta keɓanta ne kawai da eidin sallan Azumi, kuma sallar laiha ta keɓanta da kasancewa ana son ayi yanka a cikinta domin neman kusanci zuwa ga Allah.
Ita ce ababen da ake yankawa na daga raƙuma, ko shanaye, ko raguna, ko awaki domin neman kusanci zuwa ga Allah Ta'ala a ranar Eidin laiha daga bayan sallar Eidi har zuwa faɗuwan ranan goma sha uku na daga watan Zul Hijjah, Allah Ta'ala Yace: (Kayi sallah ga ubangijinka kuma kayi yanka) (Alkausar: 2). Kuma haƙiƙa an fassara sallah anan da sallar Eidi, yanka kuma da laiha.
Hukuncinta:
Sunnah ce ƙarfaffa ga wanda yake da iko a gare ta, sai musulmi ya yiwa kanshi da kuma mutanen gidanshi laiha.
Kuma an shar'antawa wanda yayi niyan laiha da kada ya cire wani abu daga gashinshi da faratunshi da kuma fatarshi; tun daga ganin jaririn watan Zul Hijjah har zuwa lokacin yanka.
Sharruɗan dabbobin da za ayi laiha dasu
Kuma su ne Raguna da Awaki, ko Shanaye, ko Raƙuma, kuma laiha bata inganta da wasunsu na daga dabbobi ko tsuntsaye. kuma tinkiya ko akuya ta isarwa mutum da mutanen gidanshi, kuma mutane bakwai zasu iya tarayya a cikin shanu ɗaya ko rakumi ɗaya.
Takai shekarar da ake buƙata
Kuma shekaran da ake buƙata a cikin raguna da tumakai shi ne wata shida, a cikin Awaki kuma shekara guda, a cikin shanaye kuma shekara biyu, a cikin raƙuma kuma shekara biyar.
Dabbobin su kasance sun kuɓuta daga aibin dake a bayyane
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Dabbobi gudu huɗu ba za suyi laiha ba: Mai ido ɗaya wanda hakan ya bayyana, da mara lafiya wanda rashin lafiyar ya bayyana, da mai ɗingishi wanda ɗingishin ya nuna, da ramamme wanda bashi da maiƙo" (Annasa'i: 4370, Attirmizi: 1497).