Ɓangaren yanzu model
Darasi Gamammun hukunce-hukuncen waɗanda suke yawaita a lokacin hunturu
Ya kamata a kashe wutar da ake yawan kunna ta a lokacin hunturu gabanin bacci, hakama na'urori masu ɗumama wuri domin zasu iya haifar da gobara, Daga Abu Musa Al-Ash'ari Allah Ya kara masa yarda yace: Gobara ta cinye wani gida akan mutanenta a Madinah a cikin dare sai aka baiwa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi labarinsu, sai yace: «Lalle wannan wutar maƙiyarku ce, idan zakuyi bacci toh ku kashe ta akanku» (Bukhari: 6294, Muslim: 2016), a cikin wani hadisi kuma: "Kada ku bar wuta a gidajenku yayin da kuke bacci" (Bukhari: 6293, Muslim: 2015).
1- Zai tuna ikon Allah Mai girma da ɗaukaka wajen yadda Yake sarrafa iska; Mai sanyi da mai zafi, mai sauƙi da mai tsanani, ta kudu da ta arewa, wacce take ɗauke da ruwa da bushashshiya, da wanin haka, Allah Maɗaukakin Sarki Yace: (Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa, da sãɓãwar dare da yini, da jirãge wadaɗnda suke gudana a cikin tẽku (ɗauke) da abin da yake amfãnin mutãne, da abin da Allah Ya saukar daga sama daga ruwa, sai Ya rãyar da ƙasa da shi a bãyan mutuwarta, kuma Ya wãtsa, a cikinta, daga dukan dabba, kuma da jũyãwar iskõki da girgije hõrarre a tsakãnin sama da ƙasa; haƙĩƙa, akwaiãyõyi ga mutãne mãsu yin hankali) (Albakara: 164).
2- Zai ji tsoron kada ta kasance azaba ce daga Allah Maɗaukaki, An karɓo daga Aisha Matar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi lalle tace: Ban taɓa ganin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana kwashewa da dariya har sai anga dadashinshi ba, sai dai shi ya kasance yana murmushi ne, sai tace: kuma ya kasance idan yaga girgije ko iska ana gane hakan daga fuskarshi, sai tace: Ya Manzon Allah naga mutane idan suka ga hadari ko girgije sai suyi farin ciki tsammanin akwai ruwa a cikinshi, sai naga kai kuma idan ka ganshi sai aga alaman tashin hankali a fuskarka! tace, sai yace: Ya ke Aisha bani da tabbacin cewa babu azaba a cikinshi, domin anyiwa wasu mutane azaba da Iska, kuma wasu mutane sun ga azaba tana zuwa sai sukace: Wannan gorgije ne wanda zai shayar damu» (Muslim: 899).
3- Zai roƙi Allah alherin dake cikinta, an karɓo hadisi daga Aisha Allah Ya kara mata yarda tace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan iska ta kaɗa yana cewa: «Ya Allah lalle ni ina roƙonKa alherinta, da alherin dake cikinta, da alherin da aka aiko ta da shi, kuma ina neman tsarinKa da sharrinta, da sharrin abunda ke cikinta, da sharrin abunda aka aikota da shi» (Muslim: 899).
4- Ya nisanci zaginta; An karɓo hadisi daga Ɗan Abbas Allah Ya kara mishi yarda lalle wani mutum ya la'anci iska a wajen Annabi (S. A. W), sai yace: Kada ka la'anci iska domin lalle ita ana bata umarni ne, kuma lalle duk wanda ya la'anci wani abun da bai cancanci la'ana ba, to la'anar zata dawo kanshi ne" (Attirmizi: 1978), a cikin wani hadisi kuma: "Kada ku zagi iska.. " (Attirmizi: 2252). Imam Ash-Shafi'i yace: "bai kamaci wani mutum da ya zagi iska ba domin lalle ita halittar Allah ce mai miShi biyayya, Kuma soja ce daga cikin sojojin Allah Ya kan iya sanya ta ta zamto Ni'ima ko azaba idan Yaso".
Daga Abdullahi Ɗan Zubair: Lalle ya kasance idan yaji tsawa sai ya bar hira, kuma yace: "Tsarki ya tabbata ga wanda tsawa take tasbihi da gode maSa, Mala'iku kuma domin tsoronShi" kuma wannan lafazin yazo a cikin Alkur'ani: {Kuma arãdu (Tsawa) tanã tasbĩhi game da gõde Masa, da malã'iku dõmin tsoronsa. Kuma Yanã aiko tsãwawwaki, sa'an nan Ya sãmi wanda Yake so da su alhãli kuwa sũ, sunã jãyayya a cikin ( al'amarin ) Allah kuma shĩ ne mai tsananin hĩla} (Arra'ad: 13).
Allah Ya wasafta ruwan sama da cewa lalle shi mai albarkah ne. Allah Maɗaukakin Sarki Yace:(Kuma Mun sauƙar da ruwa mai albarkah daga sama) (Suratu Ƙaf: 9), Kuma daga cikin ababen da akeyi yayin sauƙan ruwan sama: 1- Mutum zai yaye wani ɓangaren jikinshi domin ruwan ya taɓa, an karɓo hadisi daga Anas Allah Ya kara mishi yarda yace: Ruwan sama ya same mu alhali muna tare da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ɗan yaye tufafinshi domin ruwan ya taɓa shi, sai mukace: Ya Manzon Allah me yasa ka aikata hakan? sai yace: Lalle shi bai daɗe da barin ubangijinshi Maɗaukaki ba) (Muslim: 898)
2- Zai yi Addu'a, Kuma yazo a cikin da yawa daga asari cewa lalle lokacin sauƙan ruwan sama lokacin amsa addu'a ne.
Addu'o'i yayin sauƙan ruwan sama da bayan sauƙanshi.
Daga Aisha Allah Ya kara mata yarda, lalle Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan yaga ruwan sama yana cewa: "Ya Allah marka marka mai amfani" (Bukhari: 1032). Marka-Marka: Shi ne ruwan sama mai yawan gaske mai kwararowa.
Kuma yayi addu'ar kasancewan ruwan mai amfani ne; domin lalle ruwan sama zai iya kasancewa mai yawa amma kuma babu wani amfani a tattare da shi, yazo a cikin hadisi cewa: (Fari ba shi ne rashin ruwan sama ba, sai dai fari shi ne ruwa yayi ta sauƙa amma kuma ƙasa ba za ta tsirar da komai ba" (Muslim: 2904). Fari kuma: Shi ne tsananin rashin ruwan sama.
3- Kuma an sunnanta faɗin "Rahama" yayin sauƙan ruwan sama; An karɓo hadisi daga Aisha Matar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi tace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan ranar iska da hadari ne ana gane hakan a fuskarshi, sai kaga yana gaba kuma yana baya, idan kuma ruwan ya sauƙa sai yayi farin ciki da shi, sai damuwa ta gushe daga gare shi, Aisha tace: sai na tambaye shi, sai yace: «Lalle ni ina tsoron kada ya kasance azaba ce aka turowa Al-ummah ta», kuma ya kasance idan yaga ruwan sama yana cewa: "Rahama" (Muslim ne ya rawaito: 899).
4- Kuma an sunnanta mutum yace yayin sauƙan ruwan sama da bayan sauƙanshi: (An mana ruwa da falalar Allah da rahamarShi), Daga Zaidu Ɗan Khalid Alhahani yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yayi mana sallar asubahi a Hudaibiyyah bayan an gama ruwan saman da ya sauƙa a cikin dare, a yayin da ya gama sai ya juyo zuwa ga mutane yace: (Shin kun san abin da Ubangijinku yace?), sai suka ce: Allah da ManzonShi ne suka sani, sai yace: (Yace: An wayi gari a cikin bayi Na akwai muminai da Ni da kuma kafurai, duk wanda yace: Anyi mana ruwa da falalar Allah da rahamarShi, wannan shi ne wanda yayi imani da Ni, Amma kuma wanda yace: An yi mana ruwa da nau'in tauraro kaza da kaza to wannan shi ne wanda ya kafurce mini yayi imani da taurari) (Bukhari: 846, Muslim: 71).
Idan ruwan sama yayi tsanani kuma akaji tsoron kada ya cutar, an so mutum yayi addu'a yana mai ɗaga hannayenshi, kuma daga cikin addu'ar da tazo a cikin hakan. "Ya Allah a kewayenmu ba a kanmu ba, ya Allah akan tsaunuka da duwatsu, da ƙoramai da kuma matsiran bishiyoyi".(Bukhari: 1014, Muslim: 879).