Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Imani da cewa Allah Shi ne Ubangiji:

Allah Mai girma da ɗaukaka shi ne ubangijin dukkan komai kuma mamallakinsu, kuma mahaliccinsu, kuma mai azurta su, A cikin wannan darasin zaka san ma'anar tauhidin ubangiji da sakamakonshi.

  • Sanin ma'anar tauhidin rububiyyah
  • Sanin sakamakon tauhidin rububiyyah 

Ma'anar Tauhidin rububiyyah:

Shi ne tabbatarwa da kuma gaskata cewa lalle Allah Ta'ala shi ne ubangijin dukkan komai kuma mamallakinsu kuma mahaliccinsu kuma shi ke azurta su, kuma shi ne mai rayawa mai kashewa, shi ne mai amfanarwa da cutarwa, wanda shi ke da umarni gaba ɗaya, kuma alheri a hannunshi yake, kuma shi mai iko ne a bisa dukkan komai, bai da abokin tarayya a cikkn waɗannan ababen. Saboda haka, Tauhidin rububiyyah shi ne kaɗaita Allah cikin ayyukanshi, hakan kuma yana kasancewa ne da ababe masu zuwa:

Lalle Allah shi kaɗai ne mahaliccin dukkanin ababen da suke cikin kauni, kuma babu wani mahalicci koma bayanShi, kamar yadda Allah Ta'ala Yace: {Allah Shi ne mahaliccin dukkan komai}[Azzumar: 62]. Amma kuma halittan da mutum ya keyi ba komai bane face juya abu daga wata siffa zuwa wata siffan, ko kuma tarawa da jerawa, ko wani abu makamancin hakan, amma ba halitta bane na gaske, kuma ba samarwa daga babu bane, kuma ba rayarwa bayan mutuwa bane.

Lalle Allah shi kaɗai ne mahaliccin dukkanin ababen da suke cikin kauni, kuma babu wani mahalicci koma bayanShi, kamar yadda Allah Ta'ala Yace: {Allah Shi ne mahaliccin dukkan komai}[Azzumar: 62]. Amma kuma halittan da mutum ya keyi ba komai bane face juya abu daga wata siffa zuwa wata siffan, ko kuma tarawa da jerawa, ko wani abu makamancin hakan, amma ba halitta bane na gaske, kuma ba samarwa daga babu bane, kuma ba rayarwa bayan mutuwa bane.

Kuma lalle Allah shi ne mai azurta dukkanin halittu, babu wani mai azurtawa sai Shi, kamar yadda Allah Yace: {Kuma babu wata dabba da take doron ƙasa face arzikinta yana ga Allah} [Hud: 6]

Kuma lalle Allah shi ne mai azurta dukkanin halittu, babu wani mai azurtawa sai Shi, kamar yadda Allah Yace: {Kuma babu wata dabba da take doron ƙasa face arzikinta yana ga Allah} [Hud: 6]

Kuma cewa lalle Shi ne mamallakin dukkan komai, kuma babu wani mamallaki na haƙiƙa koma bayanShi. Allah Mai girma da ɗaukaka Yace: {Mulkin sammai da ƙasa da ababen da suke cikinsu na Allah ne} [Alma'idah: 120].

Kuma cewa lalle Shi ne mamallakin dukkan komai, kuma babu wani mamallaki na haƙiƙa koma bayanShi. Allah Mai girma da ɗaukaka Yace: {Mulkin sammai da ƙasa da ababen da suke cikinsu na Allah ne} [Alma'idah: 120].

Kuma Shi ne mai gudanar da dukkan komai, babu wani mai gudanarwa sai Shi, kaman yadda Allah Ta'ala Yace: {Shi yake gudanar da al'amura daga sama zuwa ƙasa} [Alsajadah: 5].

Kuma Shi ne mai gudanar da dukkan komai, babu wani mai gudanarwa sai Shi, kaman yadda Allah Ta'ala Yace: {Shi yake gudanar da al'amura daga sama zuwa ƙasa} [Alsajadah: 5].

Gudanarwar Allah Da Gudanarwan Mutum

Amma Gudanarwar mutum ga sha'anin rayuwarshi da tsara shi yana da alaƙa ne da abunda yake hannunshi da ababen da ya mallaka da kuma ababen da zai iya aikatawa, kuma zai iya samun nasara cikin wannan gudanarwar kuma zai iya samun cikas, amma kuma gudanarwar Allah Mai girma da ɗaukaka gamamme ne babu abunda yake fita daga cikinshi, kuma abun zantarwa ne babu abunda ya isa ya hana shi faruwa. Kaman yadda Allah Yace: {Ku saurara, lalle halitta tashi ce kuma umarni ma nashi ne, albarkan Allah ubangijin talikai ya yawaita} [Al'A'araf: 54].

Mushirkan Larabawa na zamanin Manzon Allah sun tabbatar da rububiyyar Allah:

Kafuran zamanin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sun tabbatar da cewa Allah Shi ne Mahalicci, Mamallaki, Mai gudanarwa, Allah Ta'alah Yace: {Kuma idan ka tambaye su waye ya halicci sammai da ƙasa zasuce Allah ne} [Luƙuman: 25], kuma wannan kaɗai bai shigar dasu musulunci ba; domin basu kaɗaita Allah da Ibadah ba, sai dai sun bauta wa wani tare da Shi. Duk wanda ya tabbatar da cewa Allah Shi ne ubangijin talikai -ma'ana Mahaliccinsu da Mamallakinsu, da Mai rainonsu da ni'imominShi- dole ne ya kaɗaita Allah shi kaɗai da ibadah, kuma ya gudanar miShi shi kaɗai ba tare da abokin tarayya ba.

Ta yaya hankali zai kama cewa mutum ya tabbatar da cewa lalle Allah Shi ne Mahaliccin komai kuma Shi ne Mai gudanar da kauni, Mai rayawa Mai kashewa, sa'annan ya gudanar da wani nau'i na ibadah ga waninShi?! wannan shi ne mafi munin zalumci da mafi girman zunubi, saboda hakane Luƙuman yace wa ɗanshi yayin da yake yi mishi nasiha kuma yake shiryar da shi: {Ya ɗa na kada kayi shirka da Allah, domin lalle shirka zunubi ne mai girman gaske} [luƙuman: 13].

Kuma yayin da aka tambayi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: Wana zunubi ne yafi girma a wajen Allah? sai yace: "Shi ne ka sanyawa Allah kishiya bayan shi ya halicce ka" [Bukhari: 4477, Muslim: 86].

Imani Da Rububiyyar Allah Yana Natsar Da Zuciya:

Idan bawa ya samu tabbacin cewa babu wani daga cikin halittu wanda ya isa ya fita daga cikin ƙaddarar Allah Maɗaukaki; domin lalle Allah Maɗaukaki Shi ne Mahaliccin su gaba ɗaya, babu wani mahalicci sai shi, kuma domin Shi ne Mamallakin su Yana sarrafa su yadda yake so daidai da hikimarShi, kuma idan yasan cewa lalle dukkanin umarni yana hannun Allah Maɗaukaki, babu wani mai gudanar da kauni sai Allah Shi kaɗai, kuma ƙwayan zarra bata isa ta motsa ba sai da izininShi, kuma ba zata natsu ba sai da umarninShi, kuma idan ya tabbatar da cewa lalle babu mai azurtawa sai Allah. Hakan zai gadar mishi da natsuwa a zuciyarshi, kuma zai ƙara mishi son Allah Shi kaɗai, kuma zai roƙe Shi Shi kaɗai, kuma zai nemi biyan buƙata daga gare Shi, kuma zai dogara akanShi Shi kaɗai a cikin dukkanin al'amuran rayuwarshi.

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa