Ɓangaren yanzu model
Darasi Imani Da Sunayen Allah Da Kuma SiffofinShi
Imani da sunayen Allah da kuma siffofinShi
Alkur'ani yayi matiƙan ƙarfafa alaƙar dake tsakanin bayi da Allah Ubangijinsu kuma Mahaliccinsu, kuma ya maimaita hakan a cikin ayoyi da dama; domin babu makawa dole ne sai bawa yasan waye ubangijinshi da kyawawan sunayenShi da kyawawan siffofinShi maɗaukaka waɗanda ya siffantu da su, domin ya bauta wa Allah a bisa basirah kuma yayi amfani da ma'anonin waɗannan sunayen da siffofin da kuma tasirin da suke da shi, a cikin rayuwarshi da kuma ibadarshi.
Saboda hakane musulmi zaiyi imani da abunda Allah ya tabbatarwa kanShi a cikin littafinShi ko a cikin sunnar ManzonShi (S. A. W) na daga sunaye da siffofi a bisa fiskar da ta dace da Allah Maɗaukakin Sarki.
Kuma Allah subhanahu wa ta'ala Yana da kyawawan sunaye da cikakkun siffofi, kuma bai da kwatankwaci a cikin sunayenShi da siffofinShi. Allah Ta'ala Yace {Wani abu bai zamto tamkar shi ba, kuma shi mai ji ne mai gani} [Alshura: 11]. Saboda haka Allah Maɗaukaki ya tsarkaka daga kama da wani daga cikin halittunshi a cikin dukkanin sunayenShi da siffofinShi.
Anan ne zamu bijiro da wasu daga cikin sunayen Allah Maɗaukakin Sarki
Arrahmanu Arrahimu (Mai rahama, Mai jin ƙai)
Waɗannan sunaye guda biyu da su ne Allah Ya buɗe fatihar littafinShi, kuma da su ne Allah Ya fara sanarwa bayinShi kanShi, kuma da su ne aka buɗe dukkanin surorin Alkur'ani mai girma a cikin faɗinShi: (Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai), banda suratut Taubah.
Kuma haƙiƙa ubangijinmu mai falala ne a yayin da Ya rubuta wa kanShi rahama, kuma Shi rahamarShi ta yalwaci komai da kowa, har ma rahamar dake tsakanin halittu sashinsu a bisa sashi, da rahamar da mahaifiya take da shi a bisa ɗanta, da kuma sauƙaƙewa halittu hanyar cin abinci, wannan ba komai bane face wani ɗan ƙaramin ɓangare daga cikin rahamar Allah akan halittunShi, kaman yadda Allah Yace: {Ka duba alamomin rahamar Allah yadda yake raya ƙasa bayan mutuwarta} [Rum: 50].
An karɓo daga Umar Ɗan Khaɗɗabi Allah Ya kara mishi yarda: «An kawowa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bayi, sai ga wata mata a cikinsu tana tatsan nononta tana shayarwa, idan taga wani jariri a cikin bayin sai ta ɗauke shi ta manna shi a cikinta ta shayar da shi, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace mana: shin kuna ganin cewa wannan matar zata iya jefa ɗan cikinta a wuta? sai mu kace: A'a, alhalin kuma zata iya barinshi, sai yace: Na rantse Allah Yafi jin tausayin bayinShi fiye da wannan matar ga yaronta» [Bukhari: 5999, Muslim: 2754].
Saboda haka rahamar Allah Mai girma da ɗaukaka abu ne mai girman gaske, kuma ya wuce tunanin mutum ko kimantawarshi, da ace bayin Allah sun san kimanin rahamar Allah mai girma da ɗaukaka da babu wanda zai ɗebe tsammani daga rahamarSa.
Kuma rahamar Allah Maɗaukaki nau'i biyu ne:
Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Babu wanda zai shiga Aljannah da ayyukanshi" sai sukace: Har kai ma ya Manzon Allah?! sai yace: Har ni ma sai dai idan Allah ya nitsar dani a cikin rahamarSa" [Bukhari: 6467, Muslim: 2818].
Kuma bawa a duk lokacin da biyayyarshi ta yawaita kuma kusancinshi ga Allah ya ƙaru, rabonshi na daga cancantan wannan rahamar ma sai ya ƙaru, kaman yadda Allah Ta'ala Yace: {Lalle rahamar Allah tana kusa da masu kyautatawa} [Al-A'arafi: 56].
Mai Yawan Ji Mai Yawan Gani:
Allah Mai girma da ɗaukaka yana jin dukkanin sautuka a bisa saɓanin yaruka da kuma banbancin buƙatu, koda ace an bayyana zance ne ko kuwa an ɓoye shi, a yayin da wasu jahilai sukayi tsammanin cewa lalle Allah baya jin sirrukansu da kuma zantukansu na ɓoye, sai faɗin Allah Mai girma da ɗaukaka ya sauƙa yana mai tsawata musu: {Ko suna tsammanin cewa ba Ma jin sirrukansu da kuma gulmace-gulmacensu ne, ba haka bane Manzanninmu suna nan a tattare dasu kuma suna rubutawa} [Azzukhruf: 80].
Kuma Allah subhanahu wa ta'ala yana ganin dukkanin komai koda ace ɗan mitsitsi ne, babu wani abunda yake ɓoyuwa a gare shi, kuma haƙiƙa Annabi Ibrahim alaihis salam ya yiwa mahaifinshi inkarin bautar gunkin da baya ji kuma baya gani, sai yace: {Ya kai baba na meye yasa zaka bautatawa abunda baya ji baya gani kuma bazai iya amfanar da kai da komai ba} [Maryam: 42].
To idan bawa yasan da cewa lalle Allah Mai yawan ji ne Mai yawan gani ne, babu wani abunda yake ɓoyuwa a gare shi ko da ƙwayan zarra ne a cikin sammai da ƙassai, kuma lalle cewa shi Allah Ya san sirri da ma abunda yafi sirrin ɓoyuwa, to hakan zai gadar masa da sanin cewa Allah Yana ganinshi a duk inda yake, daga nan zai kare harcenshi daga faɗawa cikin ƙarya da munanan zantuka, kuma zai kiyaye gaɓɓansa, zai kuma kiyaye zuciyarsa daga fiskantar duk wani abunda zai fusata Allah Mai girma, kuma zaiyi amfani da waɗannan ni'imomin cikin ababen da Allah Yake so ya kuma yarda dasu; domin lalle shi yana ganin sirrinshi da zahirinshi da kuma baɗininshi, saboda hakane Manzon Allah (S. A. W) yace: "Kyautatawa shi ne ka bautawa Allah tamkar kana ganinShi, domin idan kai ka kasance baka ganinShi to Shi yana ganinka" [Bukhari: 4777, Muslim: 9].
Allah subhanahu wa ta'ala yana da cikakkiyar rayuwa wacce rashi bai rigaye ta ba kuma bazata taɓa gushewa ko ƙarewa ba har abada, kuma babu wani naƙasu ko wani aibi a tattare da ita, domin ubangijinmu Ya girma kuma ya ɗaukaka daga hakan, rayuwa ce wacce take lizimtar cikakkun siffofinshi na daga sani da ji da gani da iko da iradah da sauransu na daga siffofinshi Mai girma da ɗaukaka, kuma duk wanda ya kasance wannan shi ne sha'aninsa, to babu shakka ya cancanci a bauta mishi, ayi mishi ruku'u, kuma a dogara akanshi, kaman yadda Allah Ta'ala Yace: {Kuma ka dogara akan rayayye wanda baya mutuwa} [Alfurƙan: 58].
Kuma ma'anar sunan Allah Mai tsayuwa da kanShi tana nuni zuwa ga ababe biyu:
Shiyasa haɗuwan waɗannan manyan sunayen guda biyu a waje ɗaya yana da tasiri na musamman wajen addu'a da kuma ƙasƙantar da kai zuwa ga Allah, kuma ya kasance daga cikin Addu'arshi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: "Ya Hayyu ya Ƙayyum bi rahmatika astagisu" (Ya Kai rayayya wanda yake tsaye da kanshi, ina neman agaji da rahamarka) [Attirmizi: 3524].