Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Falalan Makkah Almukarramah da Masallacin Harami

Makkah Almukarramah tana nan ne ta yammacin yankin larabawa, kuma a cikinta ne Masallacin Harami yake; Mafi tsarkakan ɗaki a doron ƙasa, kuma wannan gari mai tsarki da masallacinshi suna da matsayi mai girman gaske a cikin musulunci. A cikin wannan darasin zaka san wani abu daga cikin hakan:

  • Sanin falalan Makkah Almukarramah
  • Sanin falalan Masallacin Harami

Falalan Makkah Almukarramah: Wannan tsarkakakken gari yanada matsayi mai girman gaske da falala masu yawa, daga cikinsu akwai:

1. Ita ce mafi soyuwan gari zuwa ga Allah Ta'ala da kuma ManzonShi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi:

Abdullahi Ɗan Adiy Ɗan Alhamra Allah Ya kara mishi yarda yace: Naga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana tsaye a Alhazurah (Sunan wani wuri ne a garin Makkah) sai yace: Na rantse da Allah lalle ke ce mafi alherin ƙasar Allah, kuma ke ce mafi soyuwan ƙasar Allah zuwa ga Allah, kuma ba don an fitar dani daga gare ki ba da ban fita ba" (Attirmizi: 3925), a cikin wata riwaya kuma: "kuma ke ce mafi soyuwan ƙasar Allah a gare ni" (Ibnu Majah: 3108).

2. Lalle ita haramin Allah ne

Lalle Allah Ya haramtawa bayinShi da su zubar da jini a cikinta, ko su zalumci wani a cikinta, ko a farauci dabbobin ta, ko a yanki wani abu na daga bishiyoyinta da ciyayinta. Allah Mai girma da ɗaukaka Yace: (Lalle an umarce ni ne da na bautawa ubangijin wannan garin wanda ya haramta ta, kuma Shi Yanada komai, kuma an umarce ni da na kasance daga cikin Musulmai) (Alnaml: 91).

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Lalle Makkah Allah ne Ya haramta ta ba mutane ba, saboda haka baya halatta ga mutumin da yayi imani da Allah da ranan ƙarshe da ya zubar da jini a cikinta, kuma kada ya sare wata bishiya a cikinta" (Bukhari: 104, Muslim: 1354).

3. Lalle a cikinta ne Masallacin Harami yake, kuma wannan Masallacin yana da falala masu yawa, daga cikinsu:

1. Lalle shi ne farkon Masallacin da aka gina shi domin ibadan Allah a doron ƙasa:

Babban sahabi Abu Zarril gifari Allah Ya kara mishi yarda yace: Ya Manzon Allah! Wana masallaci ne aka fara ginawa a doron ƙasa? sai yace: «Masallacin Harami» nace: sai wanne? yace: «Masallacin ƙudus» sai nace: Shekara nawa a tsakanin su? yace: «Shekaru arba'in, amma kuma duk wurinda sallah ta riske ka toh kayi sallah domin wurin masallaci ne» (Bukhari: 3366, Muslim: 520).

2. A cikinta akwai Ka'abah mai darajah:

Ka'abah ita ce wannan ginin da yake tsakiyan farfajiyar Masallacin Harami, kuma ita ce Alkiblar da musulmai suke fiskanta daga dukkanin sassan duniya yayin sallarsu gaba ɗaya. Annabi Ibrahim badaɗen Allah da ɗanshi isma'il alaihimus salam ne suka gina ta da umarnin Allah Mai girma da ɗaukaka, sa'annan sai aka sabanta gininshi sau da dama daga baya. Allah Maɗaukaki Yace:(A lokacin da Ibrahim yake ɗauke da ginshiƙi na daga ɗakin Ka'abah yana cewa Ya Allah Ka karɓa daga garemu, domin lalle Kai ne mai yawan ji Mai yawan sani) (Albakara: 127). Kuma Ƙuraishawa sun yarda da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance wanda zai sanya hajarul aswadu a filinshi yayin da suka sake gina ta.

3. Ana ruɓanya ladan salloli a cikinta:

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Sallah guda ɗaya a cikin wannan masallacin nawa yafi salloli guda dubu a cikin waninshi saidai Masallacin Harami, kuma sallah a Masallacin Harami yafi salloli dubu ɗari a cikin waninshi". (Ibnu Majah: 1406, Ahmad: 14694).

4. Allah Ya farlanta hajjin ɗakinShi mai alfarma ga wanda ya samu ikon tafarki zuwa gare shi:

Haƙiƙa Annabi Ibrahim alaihis salam ya ƙira mutane zuwa ga aikin hajji, sai mutane suka amsa mishi daga kowane waje, sai Annabawa sukayi aikin hajji zuwa gare ta kaman yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba da labari, Allah Ta'ala Yace Yana Mai ba da labarin umarninShi ga Amnabi Ibrahim: (Kuma kayi yekuwa a cikin mutane da aikin hajjj, zasu zo maka suna masu tafiya da ƙafa, kuma akan kowana ramammen rakumi, lalle su masu zuwa ne daga kowana lungu mai zurfi) (Alhajj: 27).

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa