Ɓangaren yanzu model
Darasi Wankan Gawa Da Saka Mishi Likkafani
Abunda akeso a aikata yayin da musulmi ya mutu
Idan mutuwa ta tabbata kuma rai ya rabu da gangan jiki, anaso a aikata ababe da yawa, daga cikinsu
A yayin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya shiga kan Abu Salamah kuma haƙiƙa idanunshi suna buɗe sai ya rufe mishi ya kuma ce: "Idan kuka shiga kan mamatanku to ku rufe musu idanuwansu" (Ibnu Majah: 1455).
2. Haƙuri da mallakan rai
Da rashin ɗaga murya da kuka da kuma ife-ife, da baiwa mutanen mamacin da makusantanshi haƙuri, kuma lalle Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya umarci ɗaya daga cikin ƴaƴanshi yayin da ɗanta ya rasu da tayi haƙuri ta nemi lada a wurin Allah (Bukhari: 1284, Muslim: 923).
Kaman yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya aikata tare da Abu Salamah -Kuma shi yana daga cikin manyan sahabbai - yayin da ya mutu, sai yace: "lalle shi rai idan aka zare shi to idanuwa suna binshi" sa'annan sai yace: Ya Allah Ka gafartawa Abu Salamah Ka kuma ɗaga darajarshi a cikin mutane managarta, kuma Ka maye gurbin shi cikin abunda ya bari, kuma Ka gafarta mana da shi ya Ubangijin talikai, kuma Ka yalwata mishi kabarinshi, Ka kuma haskaka mishi a cikinshi" (Muslim: 920).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Ku gaggauta gawa zuwa makoncinta, idan ta kasance ta gari ce, to kuna gabatar da ita zuwa ga alheri ne, idan kuma koma bayan hakane, to sharri ne kuke ɗauke dashi akan kafaɗunku" (Bukhari: 1315, Muslim: 944).
5. Taimakawa mutanen mamaci
Da taimakonsu wajen gudanar da wasu uzurinsu, kuma lalle Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yayi umarni da a dafawa mutanen ɗan baffanshi Ja'afar Binu Abi Ɗalib Abinci yayin da aka kashe Ja'afar Allah Ya kara mishi yarda, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: "Ku dafawa mutanen Ja'afar abinci domin lalle abunda zai shagaltar dasu yazo musu" (Abu Dawood: 3132, Attirmizi: 998, kuma Ibnu Majah ya inganta shi 1610).
Wajibi ne a wanke mamaci gabanin a saka mishi likkafani a kuma binne shi, kuma wani daga cikin mutanenshi ko makusantanshi ne zai wanke shi ko kuma waninsu daga cikin musulmai, domin lalle an wanke Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bayan ya rasu kuma shi ne tsarkakakke mai tsarkakewa.
A yayin wanke gawa za a jiƙa dukkanin jikinshi da ruwa, kuma za a kawar da najasa idan har akwai ta, tare da kula da suturta Al'auranshi yayin wankan. Kuma anaso a kula da ababe masu zuwa:
1. A suturta Al'auranshi wato abunda ke tsakanin cibiyarshi da gwiwanshi, bayan tuɓe mishi kayanshi.
2. Mai wanke gawa zai sanya safar hannu a hannayenshi, yayin da yake wanke Al'auran mamacin.
3. Zai fara ne da kawar da najasa da ƙazanta daga gawar idan har akwai su.
4. Sa'annan sai ya wanke gaɓoɓin alwala a bisa tsarin da aka saba.
5. Sa'annan sai ya wanke kai da sauran gangan jiki, kuma an so ya wanke shi da ganyen magarya ko sabulu, daga nan kuma sai ya kwara mishi ruwa.
6. Anso da ya fara wanke gefenshi na dama sa'annan na hagu.
7. Kuma anso a maimaita wankewa har sau uku ko fiye da haka idan akwai buƙatar hakan.
Kaman yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya gayawa matan da suka kasance suna wanke ƴarshi Zainab Allah Ya kara mata yarda: "Ku wanke ta sau uku ko sau biyar ko fiye da haka idan kunga akwai buƙatan hakan" (Bukhari: 1253, Muslim: 939).
8. Za a iya saka wani ƙelle ko Auduga ko wani abu makamancinsu
A dubura, da gaba, da kunnuwa biyu, da hanci da baki; domin kada wata najasa ko jini ya fito daga gare su.
Yayin wanke shi da bayan wanke shi, domin lalle Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yayi umarni ga matan da suka kasance suna wanke ƴarshi Zainab da su sanya Kafur a cikin ruwan wanke ta na ƙarshe (Kafur wani nau'i ne na turare)(Bukhari: 1253, Muslim: 939).
Waye zai wanke mamaci?
Kuma Aisha Allah Ya kara mata yarda tace: «Da ace na fiskanta lamari na kaman abunda na juyawa baya da babu wanda zai wanke Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi face matanshi» (Abu Dawood: 3141, Ibnu Majah: 1464).
Sanyawa mamaci likkafanin da zai suturta shi yana daga cikin haƙƙokanshi waɗanda suke wajbi akan mutanenshi da kuma musulmai, kuma hakan farilla ce wanda wani yakan ɗaukewa wani, domin faɗin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi "Ku sanya daga cikin tufafinku farare saboda fari na daga cikin mafificin kayanku, kuma ku sanya mamatanku ma a ciki" (Abu Dawood: 3878).
Kuma ana ɗaukan kuɗaɗen da za ayi sungullan suturta mamaci ne daga abubda ya bari idan ya kasance mai dukiya ne, idan kuma ya kasance bai bar wani abu na daga dukiya ba, to sungullan tufatar dashi ya wajaba akan waɗanda kulawa da shi ya zamto wajibi a gare su yayin da yake raye, kaman babanshi, da kakanshi, da ɗanshi, da jikanshi, idan kuma ya kasance dukkansu basu da hali, to nauyin ya koma kan mawadata daga cikin musulmai.
Abunda yake wajibi na likkafani ga mamaci shi ne abunda zai suturta mishi jikinshi na daga tsarkakakken tufafi, mamacin ya kasance na miji ne ko ta mace.