Ɓangaren yanzu model
Darasi Falalan Alkur'ani Mai Girma:
Alkur'ani mai girma yanada manya-manyan falala kuma masu yawan gaske, daga cikinsu akwai masu zuwa:
Daga Usman Bin Affan Allah Ya kara mishi yarda, daga Annabi (S.A.W) yace: «Mafi alherinku shi ne wanda ya koyi Alkur'ani ya kuma koyar da shi» [Bukhari: 5027].
Daga Anas Bin Malik Allah Ya kara mishi yarda, daga Annabi (S. A. W) yace: «Lalle Allah Yana da iyali daga cikin mutane» sai sukace: ya Manzon Allah, su waye waɗannan? sai yace: Ma'abota Alkur'ani su ne iyalan Allah kuma makusantan Shi». [Ibnu Majah: 215]».
Daga Abdullahi Bin Mas'ud Allah Ya kara mishi yarda yace, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Duk wanda ya karanta harafi ɗaya daga littafin Allah yanada kyakkyawan aiki ɗaya, kuma kowace kyakkyawa za a ninkata sau goma, bance Alif. Lam. Mim shi ne harafi ɗaya ba fah, saidai Alif harafi ne, lamun harafi ne, mimun ma wani harafi ne» Tirmizi ne ya rawaito [2910].
4. Sauƙan Mala'iku da natsuwa da rahama a wuraren da ake tilawar Alkur'ani ko ake darasunshi.
Daga Abu Hurairah Allah Ya kara mishi yarda yace, lalle Manzon Allah (S. A. W) yace: «Wasu mutane ba zasu taru a cikin wani ɗaki daga cikin ɗakunan Allah, suna karanta littafin Allah kuma suna mudarasarshi a tsakaninsu ba face natsuwa ta sauƙa a gare su, rahama ta lulluɓe su, kuma mala'iku su kewaye su, Allah kuma Ya ambace su a cikin waɗanda suke wurinshi» [Muslim: 2699].
5. Ceton Alkur'ani ga ma'abotanshi
Daga Abu Umamatal Bahili Allah Ya kara mishi yarda yace: Naji Manzon Allah (S. A. W) yana cewa: «Ku karanta Alkur'ani domin lalle shi zai zo a ranar alkiyama yana mai ceto ga ma'abotanshi» [Muslim: 804].
Daga Aisha Allah Ya kara mata yarda tace: Manzon Allah (S. A. W) yace: «Gwani a cikin Alkur'ani yana tare da mala'iku masu girma a wurin Allah, wanda kuma yake karanta Alkur'ani kuma yana in'ina a cikinshi kuma yana bashi wahala, toh yana da lada biyu» [Muslim: 798].
7. Alkur'ani yana ɗaga darajar ma'abocinshi:
Daga Umar Binul Khaɗɗab Allah Ya kara mishi yarda, lalle Manzon Allah (S. A. W) yace: «Lalle Allah Yana ɗaga wasu mutane da wannan littafin kuma yana ƙasƙantar da wasu» [Muslim: 817].
Daga Abdullahi Bin Amru Binul Ãs Allah Ya kara musu yarda yace: Manzon Allah (S. A. W) yace: «Za a gayawa ma'abocin Alkur'ani: Ka karanta ka hau, kuma ka karanta shi tamkar yadda kake karantawa a cikin duniya, domin masauƙinka shi ne wurin ƙashen ayar da ka karanta» [Abu Dawood: 1464].
9. Ma'abocin Alkur'ani za a sanya mishi riga da hulan sarauta na karama ranan Alkiyama
Daga Abu Hurairah Allah Ya kara mishi yarda, lalle Manzon Allah (S. A. W) yace: «Alkur'ani zai zo a ranan alkiyama, sai yace: Ya ubangiji ka ƙyawata shi, sai a sanya mishi hulan sarauta na karama, sa'annan sai yace: Ya Allah Ka ƙara mishi, sai a sanya mishi tufafin karama, sa'annan sai ya sake cewa: Ya Allah Ka yarda da shi, sai Allah Ya yarda dashi, sai ace da shi: ka karanta kuma ka hau sai a kara mishi kyakkyawan aiki da kowace ayah» [Attirmizi: 2915].
10. Allah Mai girma da ɗaukaka zai karrama iyayen ma'abocin Alkur'ani da manya-manyan nau'ukan girmamawa
Daga Sahal Bin Mu'az daga babanshi Allah Ya kara musu yarda, lalle Manzon Allah (S. A. W) yace: «Duk wanda ya karanta Alkur'ani ya kuma yi aiki da shi, za a sanyawa iyayenshi wani kan sarki ranan alkiyama, wanda haskenshi yafi hasken rana a cikin duniya da ta kasance a cikinku, toh ya kake zaton wanda kuma yayi aiki da wannan?!» [Abu Dawood: 1453].
11. Haddace Alkur'ani da karantar da shi yafi duniya da abin da ke cikinta
An karɓo daga Uƙbata Bin Ãmir Allah Ya kara mishi yarda yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fito alhali muna Suffah, sai yace: «Waye daga cikinku zai so yayi sammako a kowace rana zuwa Baɗhan, ko kuma zuwa Aƙiƙ, sai ya dawo da raƙuma guda biyu masu ciki ba tare da ya aikata wani zunubi ba, kuma ba tare da ya yanke zumunci ba?» sai mukace: ya Manzon Allah muna son hakan, sai yace: «shin ɗayanku ba zaiyi sammako zuwa masallaci ya koyi ko ya karanta ayoyi biyu daga littafin Allah Maɗaukaki, yafi mishi alheri daga raƙuma biyu masu ciki, ayayi uku kuma sunfi rakuma uku, ayoyi huɗu sunfi rakuma huɗu da kuma adadinsu na daga rakuma [Muslim: 803].