Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Hukunce-hukunce da kuma ladduban karanta Alkur'ani

Alkur'ani mai girma maganan Allah Mai girma da ɗaukaka ne, kuma ya wajaba akan duk wani wanda zai karanta shi da ya san hukunce-hukuncen shi da kuma ladduban shi. a cikin wannan darasin zaka san wasu daga cikin waɗannan hukunce-hukuncen da kuma ladduban.

Sanin hukunce_hukunce da kuma ladduban karatun Alkur"ani

Hukuncin Haddace Alkur'ani

١
Malamai suyi Ijma'i akan cewa haddace Alkur'ani dukkaninshi da ka farilla ce wacce wasu sukan iya ɗaukewa wasu, idan wasu adadi masu yawa na daga musulmai suka haddace shi to sun ɗaukewa sauran, kenan ko su basu haddace ba babu zunubi akansu.
٢
Kuma ya wajaba akan kowana musulmi da ya haddace abunda zai inganta sallarshi da shi na daga Alkur'ani, kuma ita ce Fatiha.
٣
Kuma an so musulmi ya haddace ma tayassara na daga Alkur'ani kuma ya dinga karawa, saboda akwai falala mai girma da kuma lada mai yawa a cikin haddar Alkur'ani.

Daga Aisha Allah Ya kara mata yarda, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Misalin wanda yake karanta Alkur'ani alhali ya gwanance a cikinshi yana tare da manyan mala'iku» [Bukhari: 4937].

Hukuncin Tilawar Alkur'ani Mai Girma

Ana so musulmi ya dinga tilawar Alkur'ani mai girma, kuma ya yawaita hakan gwargwadon ikonshi; Allah Maɗaukaki Yace: {lalle waɗanda suke tilawar littafin Allah kuma suka tsayar da Sallah, suka ciyar daga abin da muka azurtasu da shi a asirce da kuma a bayyane, suna tsammanin kasuwancin da babu asara a cikinta} [Faɗir: 29].

Hukuncin Sauraro Da kuma Natsuwa Yayin Karatun Alkur'ani

Ya wajaba akan musulmi da ya saurari karatun Alkur'ani ya kuma natsu yayin da ake karanta shi, idan hakan ya kasance a cikin sallar farillah ne, da kuma huɗubar jumma'a, saboda faɗin Allah Maɗaukaki: {Kuma idan aka karanta Alkur'ani toh ku saurare shi kuma kuyi shuru domin ku rabauta} Al-A'araf: 204].

Kuma ana son sauraron karatun Alkur'ani da natsuwa yayin karanta shi a wasu wuraren da ba wanda aka ambata ba, domin hakan girmama maganan Allah ne da kuma karrama shi.

Hukuncin Aiki Da Alkur'ani

Wajibi ne akan kowa da yayi imani da Alkur'ani mai girma, kuma yayi aiki da hukunce-hukuncen shi, ya halalta halalinshi, ya haramta haram ɗinshi, ya tsaya a wurin haninshi, kuma ya aikata ababen da yayi umarni da su.

Allah Maɗaukaki Yace: {Lalle waɗanda muka basu littafi suna karanta shi matiƙar karatunshi, waɗannan su ne waɗanda sukayi imani da shi} [Albakara: 121], Ibnu Mas'ud da Ibnu Abbas Allah Ya kara musu yarda sukace: ma'anar ita ce: suna halasta halalinshi kuma suna haramta haramun ɗinshi, kuma basa jirkita shi daga ma'anoninshi.(Tafsirin Ibn Kasir: 403/ 1].

Daga Abdullahi Bin Mas'ud Allah Ya kara mishi yarda yace: «Mun kasance idan muka koyi ayoyi goma na daga Alkur'ani a wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ba zamu koyi wasu goman da aka sauƙar a bayansu ba har sai mun san dukkanin abunda suke cikinsu» [Alhakim: 2047]. faɗinshi "Abunda suke cikinsu" ma'ana abunda ke cikinsu na daga aiki kamar yadda wani daga cikin masu rawaito hadisi ya bayyana.

Naci Da Dagiya Akan Karatun Alkur'ani Da Kuma Rashin Ƙaurace Mishi

Ya kamata akan kowana musulmi da ya nace akan karatun Alkur'ani, kuma bai kamata ace wata rana ta wuce ba tare da ya karanta wani ɓangare na Alkur'ani ba, domin kada ya manta shi ko kuma ya ƙaurace mishi, Allah Maɗaukaki Yace: {Kuma Manzon yace ya ubangiji haƙiƙa mutane na sun ɗauki wannan Alkur'anin abun ƙauracewa} [Alfurƙan: 30].

Daga Abu Musa Allah Ya kara mishi yarda, daga Annabi (S. A. W) yace: Kuyi riƙo da wannan Alkur'anin, domin na rantse da wanda rai na yake hannunshi yafi rakumi a akalanshi saurin kuɓucewa» [Bukhari: 5033].

Ladduban Karatun Alkur'ani Mai Girma

Karatun Alkur'ani yanada ladduban da ya kamata a kula da su domin karatun ya zamto karɓaɓɓe wanda za a ba da lada akanshi, daga cikin waɗancan ladduban akwai waɗanda suke kasancewa gabanin karatu, akwai kuma waɗanda suke kasancewa bayan karatun.

Ladduban Gabanin Karatun Alkur'ani Mai Girma;

١
Ya tsarkakewa Allah Karatun shi, abun nufi shi ne ya zamto yana neman yardan Allah da kuma sakamakonShi da karatun shin, domin faɗin Allah Maɗaukaki: {Kuma ba a umarce su da komai ba face da su bautatawa Allah suna masu tsarkake miShi addini} [Albayyinah: 5]. kuma wannan ladabin kamar yadda yake kasancewa gabanin karatun Alkur'ani, yana kasancewa yayin karatun Alkur'anin ma.
٢
Ya tsarkaka daga hadasi dukansu biyu, babban da ƙaramin, saboda faɗin Allah Maɗaukaki: {Babu wanda zai shafe shi saidai mai tsarki}[Alwaki'ah: 79].
٣
Yayi siwaki domin ya tsarkake bakinshi saboda hakan hanyar Alkur'ani ne, An karɓo daga Huzaifa Allah Ya kara mishi yarda: «lalle Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan ya tashi domin sallar tahajjudi a cikin dare yana goge bakinshi da asuwaki» [Bukhari: 1136, da Muslim: 255].
٤
Ya fiskanci Alƙiblah yayin karatunshi, domin ita ce mafificiyar jiha, an karɓo hadisi daga Abu Hurairah Allah Ya kara mishi yarda yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Lalle kowana abu yanada shugaba, kuma lalle shugaban majalisi shi ne fiskantar Alƙiblah» Ɗabarani ne ya rawaito (2354) da kyakkyawan isnadi.
٥
Yayi Isti'aza ma'ana ya nemi tsarin Allah daga Shaiɗan saboda faɗin Allah Maɗaukaki: {Idan zaka karanta Alkur'ani sai ka nemi tsarin Allah daga Shaiɗan jefaffe} [Alnahal: 98].
٦
Ya karanta basmalah idan ya fara karatun daga farkon surah ne, daga Anas Bin Malik Allah Ya kara mishi yarda yace: Akwai wata ranar da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance a cikinmu, sai ya sunkuyar da kanshi na wani lokaci, sa'annan sai ya ɗaga kanshi yana mai murmushi, sai mukace: menene ya saka ka dariya ya Manzon Allah? sai yace: «Ɗazu an sauƙar mini da wata Surah» sai ya karanta: Bismillahir rahmanir tahim {Inna A'aɗainakal kausar * Fa salli li rabbika wanhar * Inna shani'aka huwal Abtar} [Alkausar: 1 -3], (Muslim: 400).

Ladduban Yayin Karanta Alkur'ani Mai Girma:

١
Ya karanta Alkur'anin daki daki, abun nufi ya karanta shi da hankali cikin natsuwa, domin faɗin Allah Maɗaukaki: {Kuma ka kyautata karanta Alkur'ani daki daki} [Almuzammil: 4].
٢
Ya karanta Alkur'anin da kyautatawa, lalle an tambayi Anas Allah Ya kara mishi yarda, yaya karatun Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yake? sai yace: karatunshi ya kasance yana ja. sai ya karanta Bismillahir rahmanir rahim. ya ja bismillahi, ya ja Arrahmani, ya ja Arrahimi» [Bukhari: 5046].
٣
Kyautata sauti da karatun, an karɓo daga Barra'i Bin Ãzib Allah Ya kara mishi yarda yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Ku ƙyawata Alkur'ani da sautukanku» [Abu Dawood: 1468].
٤
Ya roƙi Allah yayin karanta ayar rahama, ya nemi tsarin Allah yayin karanta ayar azaba, yayi tasbihi yayin karanta ayar tasbihi, yazo a cikin hadisin Huzaifa da sallarshi tare da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Sa'annan ya buɗe Ali Imran sai ya karanta ta, yana karatu cikin tsanaki, idan ya wuce ayar da akwai tasbihi a cikinta sai yayi tasbihi, kuma idan yazo kan ayar roƙo sai ya roƙa, kuma idan yazo kan ayar neman tsari sai ya nemi tsarin» [Muslim: 772].
٥
Ana so yayi sujjada a yayin da yazo kan ayoyin da akwai sujjadar tilawa a cikinsu, daga Aisha Allah Ya kara mata yarda tace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana faɗa a cikin sujjadar Alkur'ani a cikin dare, yana yawan maimaita cewa «Fuskata tayi sujjada ga wanda Ya halicce ta, kuma Ya tsaga jinta da ganinta da hikimarShi da kuma ƙarfinShi» [Abu Dawood: 1414].
٦
Ya lizimci natsuwa da kwanciyan hankali da tsanaki yayin karanta Alkur'ani, Allah Maɗaukaki Yace: {Wannan littafi ne mai albarkah wanda muka sauƙar maka, domin suyi tadabburin ayoyinshi kuma domin masu hankali su hankalta} [Sad: 29].

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa