Ɓangaren yanzu model
Darasi Hukunce-hukunce da kuma ladduban karanta Alkur'ani
Hukuncin Haddace Alkur'ani
Daga Aisha Allah Ya kara mata yarda, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Misalin wanda yake karanta Alkur'ani alhali ya gwanance a cikinshi yana tare da manyan mala'iku» [Bukhari: 4937].
Hukuncin Tilawar Alkur'ani Mai Girma
Ana so musulmi ya dinga tilawar Alkur'ani mai girma, kuma ya yawaita hakan gwargwadon ikonshi; Allah Maɗaukaki Yace: {lalle waɗanda suke tilawar littafin Allah kuma suka tsayar da Sallah, suka ciyar daga abin da muka azurtasu da shi a asirce da kuma a bayyane, suna tsammanin kasuwancin da babu asara a cikinta} [Faɗir: 29].
Hukuncin Sauraro Da kuma Natsuwa Yayin Karatun Alkur'ani
Ya wajaba akan musulmi da ya saurari karatun Alkur'ani ya kuma natsu yayin da ake karanta shi, idan hakan ya kasance a cikin sallar farillah ne, da kuma huɗubar jumma'a, saboda faɗin Allah Maɗaukaki: {Kuma idan aka karanta Alkur'ani toh ku saurare shi kuma kuyi shuru domin ku rabauta} Al-A'araf: 204].
Kuma ana son sauraron karatun Alkur'ani da natsuwa yayin karanta shi a wasu wuraren da ba wanda aka ambata ba, domin hakan girmama maganan Allah ne da kuma karrama shi.
Wajibi ne akan kowa da yayi imani da Alkur'ani mai girma, kuma yayi aiki da hukunce-hukuncen shi, ya halalta halalinshi, ya haramta haram ɗinshi, ya tsaya a wurin haninshi, kuma ya aikata ababen da yayi umarni da su.
Allah Maɗaukaki Yace: {Lalle waɗanda muka basu littafi suna karanta shi matiƙar karatunshi, waɗannan su ne waɗanda sukayi imani da shi} [Albakara: 121], Ibnu Mas'ud da Ibnu Abbas Allah Ya kara musu yarda sukace: ma'anar ita ce: suna halasta halalinshi kuma suna haramta haramun ɗinshi, kuma basa jirkita shi daga ma'anoninshi.(Tafsirin Ibn Kasir: 403/ 1].
Daga Abdullahi Bin Mas'ud Allah Ya kara mishi yarda yace: «Mun kasance idan muka koyi ayoyi goma na daga Alkur'ani a wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ba zamu koyi wasu goman da aka sauƙar a bayansu ba har sai mun san dukkanin abunda suke cikinsu» [Alhakim: 2047]. faɗinshi "Abunda suke cikinsu" ma'ana abunda ke cikinsu na daga aiki kamar yadda wani daga cikin masu rawaito hadisi ya bayyana.
Ya kamata akan kowana musulmi da ya nace akan karatun Alkur'ani, kuma bai kamata ace wata rana ta wuce ba tare da ya karanta wani ɓangare na Alkur'ani ba, domin kada ya manta shi ko kuma ya ƙaurace mishi, Allah Maɗaukaki Yace: {Kuma Manzon yace ya ubangiji haƙiƙa mutane na sun ɗauki wannan Alkur'anin abun ƙauracewa} [Alfurƙan: 30].
Daga Abu Musa Allah Ya kara mishi yarda, daga Annabi (S. A. W) yace: Kuyi riƙo da wannan Alkur'anin, domin na rantse da wanda rai na yake hannunshi yafi rakumi a akalanshi saurin kuɓucewa» [Bukhari: 5033].
Ladduban Karatun Alkur'ani Mai Girma
Karatun Alkur'ani yanada ladduban da ya kamata a kula da su domin karatun ya zamto karɓaɓɓe wanda za a ba da lada akanshi, daga cikin waɗancan ladduban akwai waɗanda suke kasancewa gabanin karatu, akwai kuma waɗanda suke kasancewa bayan karatun.