Ɓangaren yanzu model
Darasi Tarihin rayuwar Annabi Muhammadu (S. A. W) (1)
Ya wajaba akan musulmi da yasan cikakken tarihin rayuwar Annabi (S. A. W) domin ya samu damar koyi da shi a cikin dukkanin lammuranshi na rayuwa, domin tarihin rayuwanshi ya kasance aiwatar da hukunce-hukuncen musulunci ne da kuma shari'o'inshi, Allah Maɗaukaki Yace: {Haƙiƙa a cikin rayuwar manzon Allah akwai kyakkyawan abun koyi a gare ku, ga wanda ya kasance yana tsammanin saduwa da Allah da kuma ranar lahira} [Al-Ahzab: 21].
1. Dangantakanshi (S. A. W)
Dangantakan Annabi (S. A. W) shi ne mafi alherin dangantaka da kuma mafificinta. Shi ne Muhammadu Ɗan Abdullahi Ɗan Abdulmutallib Ɗan Hashim Ɗan Abdu Manafi Ɗan Ƙusayyu Ɗan Kilabi Ɗan Murrata Ɗan Ka'abu Ɗan Lu'ayyu Dan Galib Dan Fihir Dan Malik Ɗan Nadar Ɗan Kinanah Ɗan Khuzaimah Ɗan Mudrikata Ɗan Ilyasu Ɗan Mudar Ɗan Nazari Ɗan Mu'iddi Ɗan Adnan, kuma Adnan Ɗan yaron Isma'il ne amincin Allah ya tabbata a gare shi.
2. Mahaifanshi (S. A. W)
Mahaifinshi shi ne: Abdullahi Ɗan Abdulmutallib Ɗan Hashim, ya rasu alhalin yana cikin mahaifiyarshi. Mahaifiyarsa kuma ita ce: Aminatu Yar' Wahab Ɗan Abdu Manafi Ɗan Zuhrata.
3. Haihuwarshi (S. A. W)
An haife shi ranar litinin a cikin watan Rabi'ul Auwal, shekarar Giwa, wacce ta dace da shekara ta 571 Miladiyya.
4. Shayar Da shi (S. A. W)
Suwaiba kuyangar Abu Lahab ta shayar da shi na wasu kwanaki, Sa'annan sai aka shayar da shi a ƙabilar Bani Sa'ad, sai Halimatus Sadiyya ta shayar da shi, kuma ya zauna a wurinta a cikin ƙabilar Bani Sa'ad na kimanin shekaru huɗu. kuma a can ne a ka tsaga zuciyarsa, aka cire rabon son zuciya da na Shaiɗan daga gare ta, bayan nan sai Halima ta komar da shi zuwa mahaifiyarshi.
5. Rayuwarshi Da Samartakanshi (S. A. W)
Aikinshi (S. A. W) Gabanin Manzanci
Rayuwar Manzon Allah (S.A.W) gabanin manzanci ta kasance rayuwa ce mai falala da ɗaukaka, ba a taɓa sanin shi da wani shirme ba, kuma bai taɓa aikata wani laifi a cikinta ba, haƙiƙa Manzon Allah (S. A. W) ya taso a cikin kulawar Allah Maɗaukaki, kuma Allah Ya kare shi daga dauɗar jahiliyya, har saida ya kasance yafi kowa mutunci a cikin mutanenshi, kuma ya fisu kyawawan halaye, kuma ya fisu asali, kuma ya fisu kyautata maƙobta, kuma ya fisu haƙuri, kuma ya fisu gaskiya, kuma ya fisu Amana, kuma ya fisu nisantar alfasha da halayen banza, har saida ya shahara a cikinsu da "Mai gaskiya mai amana" (S. A. W).
6. Matayen Annabi (S. A. W)
Ya auri khadijah Allah Ya kara mata yarda yana da shekaru ashirin da biyar, a yayin da ya fita zuwa Sham domin yi mata kasuwanci tare da yaronta Maisara, sai Maisara yaga abunda ya bashi mamaki na daga lamarinsa, da kuma kyawawan siffofin da yake da su na gaskiya da kuma amana, to a yayin da ya dawo sai ya baiwa khadijah labarin abunda ya gani, sai ta bijirar mishi kanta da ya aure ta, kuma ita ce farkon matar da Manzon Allah (S. A. W) ya aura a rayuwarshi, kuma bai auri wata mata akanta ba har ta rasu, kuma ita ce uwar dukkanin yaranshi, sai dai Ibrahim, kuma Khadijah Allah Ya kara mata yarda ta rasu ne gabanin hijirah da shekaru uku.
Sunayen Matan Annabi (S. A. W)
7. Yaran Annabi (S. A. W)
Ƴaƴan Annabi (S. A. W) a bisa zance mafi inganci guda bakwai ne: (Uku Maza, huɗu Mata).
Ƴaƴanshi Maza guda uku ne: Al-Kasim, da shi ne ake mishi alkunya, kuma ya rayu ne na wasu ƴan kwanaki, da Abdullahi, kuma ana mishi laƙabi da Aɗɗahir da Aɗɗayyib, sai kuma na ukun su Ibrahim.
Ƴaƴa matanshi guda huɗu ne: Zainab kuma ita ce babbar ƴarshi, da Ruƙayya, da Ummu Kulthum, da Fadimah. Saboda haka dukkanin yaran Annabi (S. A. W) Mazansu da Matansu uwar muminai Khadijah Allah Ya kara mata yarda ce ta haife su, sai dai Ibrahim domin shi mahaifiyarshi kuyangar Annabi ce mai suna Mariyatul Ƙibɗiyyah wacce Al-Muƙauƙis ya ba shi kyautarta.