Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Mu'amalan mumini tare da Annoba

Yanayin mu'amalar musulmi tare da al'amuran rayuwa -Daga cikinsu kuma akwai Annoba da masifu- ya bambanta da na waninshi, kuma yana bambanta a cikinsu ne da imaninshi. Wannan darasin yana bayyana yanayin mu'amalan musulmi tare da Annoba.

Sanin hanyar da ta dace musulmi ya mu"amalanci annoba da ita

Imani da Ƙaddara

Zamuyi imani da ƙaddara alherinshi da sharrinshi domin hakan rukuni ne daga cikin rukunnan imani, kuma duk abunda ya samu bayi na daga Annoba da cututtuka da masifu suna faruwa ne da hukuncin Allah da kuma ƙaddararShi; sai mu yarda da hukuncin Allah kada muyi fushi ko ƙorafi ko hayaniya. Allah Ta'ala Yace: (Babu wani masifa da zai auku sai da izinin Allah, kuma duk wanda yayi imani da Allah, Allah Zai shiryar da zuciyarshi kuma Allah Masanin dukkan komai ne) (Attgabun: 11).

Cututtuka ba sa zuwa da kansu:

Mumini yana ƙudurta cewa lalle cututtuka ba sa cutarwa da ƙarfinsu, sai dai da umarnin Allah da ƙaddarar Shi, kuma duk da haka haƙiƙa ya umarce mu da riƙo da sababin kiwo lafiya da na rigakafi na zahiri, ta hanyan nisantar ababen da suke jawo cututtuka da wuraren da annoba ta sauƙa, da kuma kula da lura da rashin cakuɗuwa da marasa lafiya. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Babu camfi babu surkulle tsubbu, amma kuma ka gudu daga kuturu kaman yadda zaka gudu daga Zaki» (Bukhari: 5707).

Shin Cututtuka da Annoba azaba ne a koda yaushe?

Cututtukan annoba azaba ne daga Allah Maɗaukaki ga kafirai da munafukai, kuma rahama ce ga muminai, ta hanyan ɗaga musu darajansu da kankare musu kura-kuransu. Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya labartawa Aisha Allah Ya kara mata yarda yayin da ta tambaye shi dangane da Annoba yace: «Lalle shi azaba ce wacce Allah yake turawa wanda Yake so, kuma lalle Allah Ya sanya ta rahama ce ga muminai, babu wani wanda zai faɗa cikin annoba, sai ya zauna a garinshi yana mai haƙuri mai neman lada, ya san da cewa babu abunda zai same shi sai dai abunda aka rubuta mishi, face ya kasance yana da kwatankwacin ladan shahidi» (Bukhari: 3474).

Amfani da shawarwarin hukumomin kula da lafiya:

Ya wajaba akan musulmi a cikin wannan yanayin da ya dinga amfani da shawarwarin hukumomin kula da lafiya, da kuma ɗaukan nauyi wajen gabatar da maslahar Al-umma akan ta shi maslahar, ya kuma ba da gudunmawa wajen samun lafiya da komawar rayuwa zuwa yadda take a baya. Allah Ta'ala Yace: {Kuyi taimakekkeniya akan biyayya ga Allah da taƙawa, kuma kada kuyi taimakekkeniya akan zunubi da ƙiyayya} (Al-Ma'idah: 2).

Ababen da aka haramta a lokacin Annoba:

1- yaɗa labaran ƙarya da kuma kambama ta

Babu shakka cewa lalle yáɗa labaran da ba gaskiya ba yana daga cikin ƙaryar da aka haramta, kuma yana daga cikin sabbuban yaɗa ɓarna a cikin mutane, saboda haka yana da Mahimmanci mutum ya kwaɗaitu a bisa rashin watsa duk wani labarin da bai da tabbaci akanshi. Allah Ta'ala Yace yayin da Yake ambatan siffofin munafukai: {Kuma idan wani lamari na daga tsaro ko tsoro ya zo musu sai su yaɗa shi, da ace sun komar da shi zuwa ga Allah, da zuwa ga Manzo, da kuma mahukunta daga cikinsu da waɗanda suke ciro hukunci daga cikinsu sun sanshi} (Annisa'i: 83).

2- Ajiyan kayan abinci

Allah Ya haramta boye abun sayarwa, da ha'inci, da ɗaga farashi, da wasa da ababen rayuwan mutane, musamman a lokutan da masifu suke faruwa, wannan yana daga cikin cin dukiya da ƙarya da ha'inci, da kuma lalata amana, da mummunar manufa. Manzon Allah (S. A. W) yace: «Duk wanda ya ɓoye wani abun sayarwa domin yayi tsada akan musulmai to shi mai laifi ne». (Almusnad 8617).

3. Sakaci wajen kamuwa da Annobar

Sakaci wajen yaɗuwan annoba daga mara lafiya zuwa mai lafiya ta kowace hanya ce haramun ne, kuma yana daga cikin manya-manyan zububai da laifi, kaman yadda ya cancanci uƙuba a duniya, kuma wannan uƙubar tana bambanta ne da yanayin girman laifi da kuma tasirinshi akan ɗaiɗaikun mutane da kuma Al-ummah gaba ɗaya.

Uƙubar wanda yake yaɗa Annoba zuwa waninshi da gangan:

١
Idan manufarshi ita ce yaɗa annoba a cikin Al-ummah, to lalle za ayi la'akarin wannan aikin nashi a matsayin ta'addanci da yaɗa ɓarna a doron ƙasa, kuma za a yanke mishi haddin ta'addanci. kamar yadda yazo a cikin aya: {Lalle sakamakon waɗanda suke yaƙan Allah da ManzonShi kuma suke tafiya da ɓarna a doron ƙasa shi ne: A kashe su, ko a gicciye su, ko a yanke hannayensu da ƙafofinsu a bisa saɓani, ko a kore su daga cikin ƙasa, lalle waɗannan taɓaɓɓu ne a cikin duniya kuma a lahira suna da azaba mai girman gaske} (Al-Ma'idah: 33).
٢
Idan kuma manufar wanda ya yaɗa annoban ta zamto cutar da wani mutum ne na musamman, sai kuma ya kamu da annobar yayi rashin lafiya har ya mutu, to za a zantar mishi da hukuncin kisa.
٣
Idan kuma manufar wanda ya yaɗa annoban ta zamto cutar da wani mutum ne na musamman, sai kuma ya kamu da annobar yayi rashin lafiya amma kuma bai mutu ba, to za a ladabtar da shi da hukuncin da ya dace da aikinshi.

4. Zagin Cuta:

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya hana zagin Zazzaɓi, Daga Jabir Ɗan Abdullahi Allah Ya kara musu yarda, lalle Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yacewa Ummu Sa'ib: «Kada ki zagi zazzaɓi, domin lalle shi yana tafiyar da kura-kuran ɗan Adam, kaman yadda ƙira take tafiyar da dauɗan ƙarfe» (Muslim: 2575).

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa