Ka ci gaba da karatu

Bakayi rajistan shiga ba
Kayi rajista yanzu a cikin dandalin Taa domin ka fara karatu da kuma bibiyan ci gabanka tare da tara maki domin samun damar shiga gasa bayan yin rajistan

Ɓangaren yanzu model

Darasi Garkuwan shari'a:

Duk da riƙo da sababi da musulmi zaiyi kaman waninshi na daga mutane, sai dai lalle shi zai sake riƙo da garkuwan shari'a na kariya da na waraka na daga cututtukan bayyane da na ɓoye. kuma wannan shi ne abunda za ka san wani abu daga gare shi a cikin wannan darasin.

Sanin garkuwan shari'a na daga cututtuka da kuma Annoba

Garkuwan shari'a:

Tare da ƙaruwar firgici a tsakanin mutane dangane da cututtuka da annoba, musulmi yayin da yake ɗaukar matakan kariya, zai kuma sake kare kansa da ingantattun matakan kariya na shari'a.

1- Komawa zuwa ga Allah

Abu na farko mai muhimmanci kuma mafi girman wanda mumini zai kare kanshi da shi a lokacin masifu da bala'i, shi ne komawa zuwa ga Allah Maɗaukaki, da neman tsari da kariya daga gare Shi don nisantar sharri. Misali, a lokacin da matar sarkin Masar ta yi yunƙurin lalata da Annabi Yusufu Alaihis Salam, sai ya ce: “Ina neman tsarin Allah” (Yusuf 23). Kuma a lokacin da Jibrilu ya bayyana ga Maryama, tsira da amincin Allah su tabbata a gare ta, sai ta ce: “Ina neman tsarin Allah Mai rahama daga gare ka.” (Maryam: 18).

2- Yawaita Addu'a:

Da ƙasƙantar da kai zuwa ga Allah da komawa zuwa gare Shi, da buƙatuwa zuwa gare Shi domin ɗage bala'i da yaye damuwa, domin addu'a ita ce garkuwan musulmi da kuma takobinshi, a yayin da bala'i ya kasance yana aukuwa ne da ƙaddarar Allah da kuma hukuncin Shi to babu abunda zai kawar da shi sai Addu'a. Manzon Allah (S. A. W) yace: «Babu abunda yake mayar da hukuncin Allah face addu'a» (Attirmizi: 2139).

3- Lizimtar Alkur'ani mai girma

Da neman waraka da shi domin lalle shi waraka ne ga kowana irin cuta na bayyane da na ɓoye {Kuma Muna sauƙarwa daga Alkur'ani abunda ya kasance waraka da kuma rahama ga muminai} (Al-Isra: 82). Kuma duk da imani, da yaƙini da gaskiya buƙatuwa zuwa waraka yana ƙaruwa domin faɗin Allah Ta'ala: {Kace shi shiriya ne da waraka ga waɗanda sukayi imani} (Fussilat: 44).

Kuma Alkur'ani dukkanin shi waraka ne, amma kuma wasu surori da wasu ayoyi falala ta musamman ta zo a dangane da su; Kaman Suratul Fatiha, da Falaƙi da Nasi, da Ayatul Kursiyyu. Ibnul Ƙayyim Allah Yayi mishi rahama yace: "Da ace mutum zai kyautata neman waraka da Suratul Fatiha, da yaga tasiri na mamaki tattare da ita wajen waraka. Kuma na zauna a garin Makkah na tsawon lokaci na kasance ina rashin lafiya kuma ban samu likita ko magani ba, sai na kasance ina yiwa kai na magani da Suratul Fatiha, sai na ga tasiri na al'ajabi tattare da ita, sai na kasance ina wasaftawa duk wani wanda yake fama da wata cuta hakan; kuma da yawa daga cikinsu sun kasance suna warkewa nan take".

4- Kiyaye salloli lokaci biyar a inda ake ƙira zuwa gare su

Musamman ma sallar Asubahi; domin faɗin Manzon Allah (S. A. W): «Duk wanda yayi sallar asubahi a cikin jama'a to yana cikin kariyar Allah» (Muslim: 657).

5- Yin Addu'a yayin ganin waɗanda bala'in ya shafa

Addu'a yayin ganin marasa lafiya da waɗanda bala'i ya same su yana daga cikin garkuwa mai mahimmanci, ya zo a cikin hadisi cewa: «Duk wanda yaga wani wanda aka jarrabe shi sai yace: Na godewa Allah Wanda Ya bani lafiya daga abunda Ya jarrabe ka da shi, kuma Ya fifita ni a bisa da yawa daga waɗanda ya halitta fifitawa, wannan bala'in ko jarrabawar ba za ta same shi ba». (Attirmizi: 3432).

6- Kiyaye ambaton Allah na safiya da na maraice

Domin lalle a cikin kiyaye ambaton Allah akwai alheri mai yawan gaske a cikin wannan duniyar da kuma lada mai girma a lahira, kuma ambaton Allah na safiya da na maraice suna daga cikin mahimman azkar ɗin da ya kamata musulmi ya kiyaye su. Domin daga cikin fa'idodinsu akwai: Yalwatan ƙirji, da natsuwar zuciya, da kasancewa tare da Allah, da kuma ambaton bawa a wajen mala'iku masu daraja.

Daga cikin Addu'o'i da kuma garkuwan shari'a:

Karanta Ayatul Kursiyyu gabanin bacci:

Yazo a cikin hadisi cewa wani ya gayawa Abu Huraira Allah Ya kara mishi yarda cewa: Idan kaje shumfuɗin baccinka ka karanta Ayatul Kursiyyu domin makiyayi daga wurin Allah ba zai gushe yana tare da kai ba, kuma Shaiɗan ba zai kusance ka ba har sai ka wayi gari, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Ya gaya maka gaskiya amma kuma shi maƙarya ci ne, wancan Shaiɗan ne» (Bukhari: 3275).

Karanta ayoyi biyu na ƙarshen Suratul Baƙara:

An karɓo daga Abu Mas'ud Allah Ya kara mishi yarda, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Wanda ya Karanta ayoyi biyu daga ƙarshen Suratul Bakara a cikin dare sun isar mishi». (Bukhari: 5008, Muslim: 808).

Yawaita Tasbihi da Istigfari:

Idan mutum ya tabbata akan tasbihi da istigfari to Allah Zai kare shi daga sharri da kuma bala'i. Allah Maɗaukaki Yace: {Kuma Allah bai kasance Mai azabtar da su ba alhali suna yin istigfari} (Al-Anfal: 33).

Wasu garkuwan shari'a na daban:

١
Daga Usman Ɗan Affan Allah Ya kara mishi yarda yace: Naji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: «Duk. wanda yace: Da sunan Allah Wanda wani abu baya cutarwa da sunanShi a cikin sama ko a cikin ƙasa kuma Shi mai yawan ji ne Mai yawan gani. Sau uku, wani bala'in ba zata ba zai same shi ba har sai ya wayi gari, kuma wanda ya faɗe ta yayin da ya wayi gari sau uku wani bala'in ba zata ba zai same shi ba har sai yayi yammaci». (Abu Dawood: 5088).
٢
Daga Abu Huraira Allah Ya kara mishi yarda yace: Wani mutum yazo wajen Annabi (S. A. W) sai yace mishi: Ya Manzon Allah Na haɗu da wata kunama ta cije ni jiya da daddare, sai yace: «Yayin da ka wayi gari da ka ce ina neman tsari da cikakkun kalmomin Allah daga sharrin dukkanin ababen da Ya halitta, da bata cutar da kai ba» (Muslim: 2709).
٣
Daga Abdullahi Ɗan Khubaib yace: Mun fita a cikin wani dare mai ruwa da kuma duhu mai tsanani muna neman Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi domin yayi mana sallah, yace: Sai na riske shi, sai yace: «Ka ce» sai ban ce wani abu ba, sai ya sake cewa: «Ka ce» sai bance wani abu ba, sai yace: «Ka ce» sai nace: Me zance: sai yace: "Kace: Ƙul huwallahu Ahad, Fakaƙi da Nasi yayin da kayi yammaci da kuma yayin da ka wayi gari sau uku za su isar maka daga dukkan komai". (Attirmizi: 3575).
٤
Daga Abdullahi Ɗan Umar Allah Ya kara musu yarda yace: Ya kasance daga cikin addu'ar Manzon Allah (S. A. W): Ya Allah lalle ina neman tsarinKa daga gushewar ni'imaKa da canzawan lafiyarKa, da bazatan uƙubarKa, da kuma dukkanin fushinKa». (Muslim: 2739).
٥
Daga Anas Allah Ya kara mishi yarda, lalle Annabi (S. A. W) ya kasance yana cewa: «Ya Allah Lalle ni ina neman tsarinka daga Zabiyanci da hauka, da kuturta da kuma munanan cututtuka». (Abu Dawood: 1554).

Haƙiƙa ka kammala wannan darasin cikin nasara


Ka fara jarrabawa