Ɓangaren yanzu model
Darasi Garkuwan shari'a:
Tare da ƙaruwar firgici a tsakanin mutane dangane da cututtuka da annoba, musulmi yayin da yake ɗaukar matakan kariya, zai kuma sake kare kansa da ingantattun matakan kariya na shari'a.
Abu na farko mai muhimmanci kuma mafi girman wanda mumini zai kare kanshi da shi a lokacin masifu da bala'i, shi ne komawa zuwa ga Allah Maɗaukaki, da neman tsari da kariya daga gare Shi don nisantar sharri. Misali, a lokacin da matar sarkin Masar ta yi yunƙurin lalata da Annabi Yusufu Alaihis Salam, sai ya ce: “Ina neman tsarin Allah” (Yusuf 23). Kuma a lokacin da Jibrilu ya bayyana ga Maryama, tsira da amincin Allah su tabbata a gare ta, sai ta ce: “Ina neman tsarin Allah Mai rahama daga gare ka.” (Maryam: 18).
Da ƙasƙantar da kai zuwa ga Allah da komawa zuwa gare Shi, da buƙatuwa zuwa gare Shi domin ɗage bala'i da yaye damuwa, domin addu'a ita ce garkuwan musulmi da kuma takobinshi, a yayin da bala'i ya kasance yana aukuwa ne da ƙaddarar Allah da kuma hukuncin Shi to babu abunda zai kawar da shi sai Addu'a. Manzon Allah (S. A. W) yace: «Babu abunda yake mayar da hukuncin Allah face addu'a» (Attirmizi: 2139).
Da neman waraka da shi domin lalle shi waraka ne ga kowana irin cuta na bayyane da na ɓoye {Kuma Muna sauƙarwa daga Alkur'ani abunda ya kasance waraka da kuma rahama ga muminai} (Al-Isra: 82). Kuma duk da imani, da yaƙini da gaskiya buƙatuwa zuwa waraka yana ƙaruwa domin faɗin Allah Ta'ala: {Kace shi shiriya ne da waraka ga waɗanda sukayi imani} (Fussilat: 44).
Kuma Alkur'ani dukkanin shi waraka ne, amma kuma wasu surori da wasu ayoyi falala ta musamman ta zo a dangane da su; Kaman Suratul Fatiha, da Falaƙi da Nasi, da Ayatul Kursiyyu. Ibnul Ƙayyim Allah Yayi mishi rahama yace: "Da ace mutum zai kyautata neman waraka da Suratul Fatiha, da yaga tasiri na mamaki tattare da ita wajen waraka. Kuma na zauna a garin Makkah na tsawon lokaci na kasance ina rashin lafiya kuma ban samu likita ko magani ba, sai na kasance ina yiwa kai na magani da Suratul Fatiha, sai na ga tasiri na al'ajabi tattare da ita, sai na kasance ina wasaftawa duk wani wanda yake fama da wata cuta hakan; kuma da yawa daga cikinsu sun kasance suna warkewa nan take".
Musamman ma sallar Asubahi; domin faɗin Manzon Allah (S. A. W): «Duk wanda yayi sallar asubahi a cikin jama'a to yana cikin kariyar Allah» (Muslim: 657).
Addu'a yayin ganin marasa lafiya da waɗanda bala'i ya same su yana daga cikin garkuwa mai mahimmanci, ya zo a cikin hadisi cewa: «Duk wanda yaga wani wanda aka jarrabe shi sai yace: Na godewa Allah Wanda Ya bani lafiya daga abunda Ya jarrabe ka da shi, kuma Ya fifita ni a bisa da yawa daga waɗanda ya halitta fifitawa, wannan bala'in ko jarrabawar ba za ta same shi ba». (Attirmizi: 3432).
Domin lalle a cikin kiyaye ambaton Allah akwai alheri mai yawan gaske a cikin wannan duniyar da kuma lada mai girma a lahira, kuma ambaton Allah na safiya da na maraice suna daga cikin mahimman azkar ɗin da ya kamata musulmi ya kiyaye su. Domin daga cikin fa'idodinsu akwai: Yalwatan ƙirji, da natsuwar zuciya, da kasancewa tare da Allah, da kuma ambaton bawa a wajen mala'iku masu daraja.
Daga cikin Addu'o'i da kuma garkuwan shari'a:
Karanta Ayatul Kursiyyu gabanin bacci:
Yazo a cikin hadisi cewa wani ya gayawa Abu Huraira Allah Ya kara mishi yarda cewa: Idan kaje shumfuɗin baccinka ka karanta Ayatul Kursiyyu domin makiyayi daga wurin Allah ba zai gushe yana tare da kai ba, kuma Shaiɗan ba zai kusance ka ba har sai ka wayi gari, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Ya gaya maka gaskiya amma kuma shi maƙarya ci ne, wancan Shaiɗan ne» (Bukhari: 3275).
Karanta ayoyi biyu na ƙarshen Suratul Baƙara:
An karɓo daga Abu Mas'ud Allah Ya kara mishi yarda, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: «Wanda ya Karanta ayoyi biyu daga ƙarshen Suratul Bakara a cikin dare sun isar mishi». (Bukhari: 5008, Muslim: 808).
Yawaita Tasbihi da Istigfari:
Idan mutum ya tabbata akan tasbihi da istigfari to Allah Zai kare shi daga sharri da kuma bala'i. Allah Maɗaukaki Yace: {Kuma Allah bai kasance Mai azabtar da su ba alhali suna yin istigfari} (Al-Anfal: 33).