Ibadu
Manufan wannan ɓangaren shi ne bayyana asalin ibadu da tabbatar da su, da kuma ƙulla alaka tsakanin ibadah da hukunce-hukuncen ta a cikin Littafin Allah mai girma da kuma sunnar Annabi mai tsarki. Kuma wannan darasin zai tattauna hukunce-hukuncen ibadun da aka kallafawa mutum tare da bayani akansu filla filla kamar yadda suka zo daga Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da kuma sahabbanshi gaba ɗaya.
Maudu'an gefe
Tsarki
Sallah ita ce rukunin musulmi na biyu bayan kalmomin shahada guda biyu, a yayin da sallar mutum ta kasance ba zata inganta ba sai da tsarki, sai ya zamto wajibi akan mutum ya fara koyan tsarki domin sallarshi ta inganta.
Sallah
Sallah ita ce ginshiƙin addini kuma ita ce abunda ake so a fara koya daga cikin ibadu, domin ita ce rukuni na biyu a cikin addini bayan kalmomin shahada; Kuma musuluncin mutum baya cika sai da tsayar da ita.
Zakkah
Zakkah ita ce rukuni na uku daga cikin rukunnan musulunci, kuma ita wajibi ne na dukiya wanda Allah Ya farlanta wa masu kuɗi domin su baiwa talakawa da mabuƙata da wasunsu na daga waɗanda suka cancanci wani kashi na musamman daga dukiyarsu domin magance matsalolinsu.
Azumi
Azumin ramadan shi ne rukuni na huɗu daga cikin rukunnan musulunci, kuma azumi ibada ne mai girman gaske, Allah Ya farlantawa musulmai kamar yadda ya farlantawa Al-ummun da suke shuɗe domin samun tsoron Allah wanda shi ne mabuɗin dukkanin alheri.
Hajji
Hajji shi ne rukuni na biyar daga cikin rukunnan musulunci, kuma ya wajaba ne akan musulmi baligi wanda yake da ikon zuwa sau ɗaya a rayuwarshi.
Mutuwa Da Jana'izah
Mutuwa ba shi ne ƙarshen lamari ba sai dai wani sabon mataki ne ga mutum, kuma ita ce farkon cikakkiyar rayuwa a lahira, kuma kaman yadda musulunci ya kwaɗaitar akan kula da haƙƙoka tun daga haihuwa haƙiƙa ya tabbatar da hukunce-hukuncen da za su kare haƙƙokan mamaci kuma zasu kula da yanayin mutanenshi da makusantanshi.